Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya amince da nada Alhaji Habu Muhammad Fagge a matsayin shugaban hukumar kula da ‘yan fansho ta jihar Kano.
Read Also:
Nadin ya fara aiki ne nan take kamar yadda gwamnan ya bayar da umarnin mikawa tare da karbar ragamar mulki cikin sa’o’i 24 da wannan sanarwar.Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar aka taba ga manema a jihar.
Alhaji Habu Fagge, wanda ya kammala karatunsaa A harkokin Kudi daga Jami’ar Abraham Lincoln, ya yi wa’adi biyu a matsayin Shugaban Hukumar karɓar haraji ta jihar kano.
Ya rike mukamai daban-daban a ma’aikatun gwamnatin jihar Kano da suka hada da daraktan kudi, daraktan tsare-tsare, bincike da kididdiga da darakta akan harkokin da suka shafi haraji.
PRNigeria hausa












