Home Labarai Zamu ɗaukaka ƙara kan wanke Oronsaye daga zargin cin hanci – EFCC

Zamu ɗaukaka ƙara kan wanke Oronsaye daga zargin cin hanci – EFCC

Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattali arzikin Najeriya zagon ƙasar EFCC ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke, na wanke tsohon shugaban ma’aikata na ƙasa daga zargin halasta kuɗin haram da suka tasamman naira biliyan biyu da hukumar ke yi masa shi da wasu.

A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook, ta ce za ta ƙalubalancin hukuncin a gaban kotun ɗaukaka ƙara.

Hukumar dai na zargin Steve Oronsaye da mutunen da ake zarginsu tare da yin amfani da wasu kamfanoni wajen karkatar da kuɗin gwamnati ta hanyar amfani da kwangilolin bogi.

Yayin da yake watsi da ƙarar, alƙalin kotun mai shari’a Inyang Ekwo ya ce hukumar EFCCn ta kasa tabbatar da zarge-zargen da take yi wa mista Oronsaye.

To sai dai a cikin sanarwar da mai magana da yawun hukumar Wilson Uwujaren ya fitar ya ce alƙalin ya yi kuskure, saboda a cewarsa bai yi la’akari da shaidun da masu ƙara suka gabatar ba, a tsawon shari’ar, tare da bahasin da ɗaya daga cikin waɗanda ake ƙarar Osarenkhoe Afe ya furta da bakinsa a gaban kotun.

A shekarar 2015 ne hukumar EFFC ta gurfanar da Mista Oronsaye tare da shugaban kamfanin Fredrick Hamilton Global Services Limited, Osarenkhoe Afe da wasu kamfanoni uku bisa zarginsu da yin amfani da wasu kamfanoni wajen karkatar da kuɗin gwamnati ta hanyar amfani da kwangilolin bogi.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp