Home Labarai Zamu ɗaukaka ƙara kan wanke Oronsaye daga zargin cin hanci – EFCC

Zamu ɗaukaka ƙara kan wanke Oronsaye daga zargin cin hanci – EFCC

Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattali arzikin Najeriya zagon ƙasar EFCC ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke, na wanke tsohon shugaban ma’aikata na ƙasa daga zargin halasta kuɗin haram da suka tasamman naira biliyan biyu da hukumar ke yi masa shi da wasu.

A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook, ta ce za ta ƙalubalancin hukuncin a gaban kotun ɗaukaka ƙara.

Hukumar dai na zargin Steve Oronsaye da mutunen da ake zarginsu tare da yin amfani da wasu kamfanoni wajen karkatar da kuɗin gwamnati ta hanyar amfani da kwangilolin bogi.

Yayin da yake watsi da ƙarar, alƙalin kotun mai shari’a Inyang Ekwo ya ce hukumar EFCCn ta kasa tabbatar da zarge-zargen da take yi wa mista Oronsaye.

To sai dai a cikin sanarwar da mai magana da yawun hukumar Wilson Uwujaren ya fitar ya ce alƙalin ya yi kuskure, saboda a cewarsa bai yi la’akari da shaidun da masu ƙara suka gabatar ba, a tsawon shari’ar, tare da bahasin da ɗaya daga cikin waɗanda ake ƙarar Osarenkhoe Afe ya furta da bakinsa a gaban kotun.

A shekarar 2015 ne hukumar EFFC ta gurfanar da Mista Oronsaye tare da shugaban kamfanin Fredrick Hamilton Global Services Limited, Osarenkhoe Afe da wasu kamfanoni uku bisa zarginsu da yin amfani da wasu kamfanoni wajen karkatar da kuɗin gwamnati ta hanyar amfani da kwangilolin bogi.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp