Home Labarai Gwamnatin Kano zata tabbatar da an aiwatar da duk wasu ayyuka da...

Gwamnatin Kano zata tabbatar da an aiwatar da duk wasu ayyuka da hukumomi masu bada tallafi na kasashen duniya ke aiwatarwa a Kano.

Gwamnatin Kano zata tabbatar da an aiwatar tare da kammala duk wasu ayyuka da hukumomi masu bada tallafi na kasashen duniya ke aiwatarwa a Kano.

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Engr Abba Kabir Yusuf, ta jaddada kudirinta na bibiyar duk wasu ayyuka da bankin duniya da sauran hukumomi masu bada tallafi ke aiwatarwa a Kano.

Tabbacin hakan ya fito ne ta bakin babban Akanta na Kano Abdulkadir Abdussalam lokacin da yake jagorantar wata ganawa da wakilan kungiyoyi da hukumomin kasashen waje wadanda ke bada tallafi.

Ganawar dai ta hada da dukkanin akantoci dake jihar da kuma masu lura da hukumomin gwamnati.

Abdussalam, ya nuna damuwarsa akan yadda wasu daga cikin ayyukan aka gaza kammalasu wanda hakan ya kawo koma baya a cigaban tattalin arzikin Kano.

Babban Akantan ya buga misali da bangarori irinsu ruwansha da ilimi da lafiya da kuma noma, da yadda kuma suke da alaka takai tsaye da gina dan Adam.

A karshen ganawar, Abdulkadir Abdussalam ya baiwa masu ruwa da tsakin tabbacin gwamnatin Kano na tsayawa tsayin daka domin amfani da tallafin dake shigowa Kano ta hanyar data dace.

Amakon daya gabatane dai Gwamna Abba Kabir Yusuf yanada Abdulkadir Abdussalam amatsayin sabon babban Akantan Kano, kafin nadin nashi dai Darakta ne a hukumar tattara haraji ta jihar Kano.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp