Home Labarai Za mu samar da sabbin wuraren kasuwanci a Kano – Abba gida-gida

Za mu samar da sabbin wuraren kasuwanci a Kano – Abba gida-gida

Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi alkawarin samar da kyakyawan wakilcin na ‘yan kasuwar jihar a majalisar zartarwa ta Kano.

Ta cikin wata sanarwar da mukaddashin mai magana da yawun gwamnan kano Hisham Habib ya aikowa PRNigeria, yace Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin ‘yan kasuwar Kano a gidan gwamnatin jihar.

Ya kuma ba su tabbacin kwamishinan kasuwanci da sauran mukamai da suka danganci yan kasuwa za su fito daga cikinsu don su sami wakilci a gwamnatinsa.

Ya ce gwamnatinsa za ta bunkasa harkokin kasuwanci a jihar, ya kuma tabbatar wa ‘yan kasuwar kudirinsa na tallafa wa harkokin kasuwanci dai-dai da zamani.

Ya ce gwamnati za ta kuma rage cunkoso a birnin kano, ta hanyar bude sabbin wuraren kasuwanci, ya kuma bukaci matasan ‘yan kasuwa da su yi amfani da damar wajen bada hadin kai don cigaban jihar kano.

A jawabinsa Mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Aminu Abdussalam, ya jaddada kokarin gwamnati na ganin an dakile matsalar cin hanci da rashawa da jami’an hukumar kula da ababen hawa ta jihar da aka fi sani da KAROTA ke yi wadanda a zamanin gwamnatin da ta shude suka yi kaurin suna wajen karbar kudi a hannun yan kasuwar.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp