Za mu samar da sabbin wuraren kasuwanci a Kano – Abba gida-gida

Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi alkawarin samar da kyakyawan wakilcin na ‘yan kasuwar jihar a majalisar zartarwa ta Kano.

Ta cikin wata sanarwar da mukaddashin mai magana da yawun gwamnan kano Hisham Habib ya aikowa PRNigeria, yace Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin ‘yan kasuwar Kano a gidan gwamnatin jihar.

Ya kuma ba su tabbacin kwamishinan kasuwanci da sauran mukamai da suka danganci yan kasuwa za su fito daga cikinsu don su sami wakilci a gwamnatinsa.

Ya ce gwamnatinsa za ta bunkasa harkokin kasuwanci a jihar, ya kuma tabbatar wa ‘yan kasuwar kudirinsa na tallafa wa harkokin kasuwanci dai-dai da zamani.

Ya ce gwamnati za ta kuma rage cunkoso a birnin kano, ta hanyar bude sabbin wuraren kasuwanci, ya kuma bukaci matasan ‘yan kasuwa da su yi amfani da damar wajen bada hadin kai don cigaban jihar kano.

A jawabinsa Mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Aminu Abdussalam, ya jaddada kokarin gwamnati na ganin an dakile matsalar cin hanci da rashawa da jami’an hukumar kula da ababen hawa ta jihar da aka fi sani da KAROTA ke yi wadanda a zamanin gwamnatin da ta shude suka yi kaurin suna wajen karbar kudi a hannun yan kasuwar.

PRNigeria hausa

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 27 minutes 45 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 9 minutes 10 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com