Home Labarai Wata babbar kotu a Abuja ta yi watsi da buƙatar DSS na...

Wata babbar kotu a Abuja ta yi watsi da buƙatar DSS na tsare Emefiele

Wata babbar kotu a Abuja ta yi watsi da buƙatar da hukumar DSS ta gabatar mata mai neman izinin ci gaba da tsare dakataccen babban bankin Najeriya, Godwin Emefile da kwanaki 14 a bisa ƙarin shaidun da tace ta tattara a kan shi.

Mai shari’a Hamza Muazu ya yi wasi da ƙarar, yana kafa hujja da saɓawa zaman kotu, tare da bayyana cewa kotun bata da hurumin sauraron buƙatar.

A ranar Talata, an samu jayayya tsakanin jami’an DSS da na hukumar kula da gidan gyaran hali ta Najeriya a kan wanda zai ci gaba da tsare Mr Emefiele bayan kotu ta bayar da belinsa.

DSS ta yi Allah-wadai da lamarin, kuma ta sha alwashin gudanar da bincike a kai.

Ita dai DSS tana zargin Emefiele da laifin mallakar bindiga da harsashi ba bisa ƙa’ida ba, zargin da kuma ya musanta.

Za a ci gaba da shari’arsa ne a ranar 14 ga watan Nuwamba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp