Home Labarai Gwamnan jihar Jigawa ya kori shugaban asibitin Gumel

Gwamnan jihar Jigawa ya kori shugaban asibitin Gumel

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ya amince da hukuncin ladabtarwa ga jagororin Babban Asibitin Gumel da ke Jihar Jigawa.

Wannan na zuwa ne bayan ziyarar bazata da gwamnan ya kai Babban Asibitin a ranar Juma’ar da ta gabata, inda ya tarar da asibitin cikin mummunan yanayi da kuma rashin bayar da kulawar lafiya ga majinyata yanda ya kamata.

Sanarwar da Mai Magana da Yawun Gwamnan, Hamisu Gumel ya sanyawa hannu, ta ce, Gwamnan ya rushe Hukumar Gudanarwar asibitin tare da ɗauke manyan jami’an asibitin inda aka mayar da su Ma’aikatar Lafiya da ke Dutse domin su jira hukuncin da ya dace da su bayan an kammala bincike.

Jami’an da abun ya shafa sun haɗa da Shugaban Asibitin, Daraktan Kula Bayar da Duba Marassa Lafiya, Daraktan Mulki, Shugaban Sashin Bayar da Magani, Shugaban Sashin Gwaje-gwaje da kuma Mai Kula da Hada-hadar Kuɗi na asibitin.

Cikin laifukan da Gwamna Namadi ya kama ana aikatawa a asibitin akwai, tursasawa marassa lafiya biyan naira 7000 domin a ɗau jinin ƴan’uwansu a ƙarawa majinyatansu, tursasawa majinyata siyan auduga, rashin samar da ruwan famfo duk da gwamnati ta bayar da kuɗin yin hakan, da kuma rashin zuwa aiki a ɓangaren shugabannin asibitin na Gumel.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp