Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan jihar Adamawa ta tabbatar da aukuwar gobara a kasuwar...

Rundunar ‘Yan Sandan jihar Adamawa ta tabbatar da aukuwar gobara a kasuwar Yola

Gobara ta lalata wasu sassan babbar kasuwar garin Yola.

Rahotannin sun bayyana cewa go barar ta tashi ne  a daren Litinin yayin da yan kasuwar ke a rufe.

Wasu majiyoyi da dama sun ce shaguna da dama ne lamarin ya shafa, sannan gobarar ta yi sanadayar a sarar kayayyakin miliyoyin Naira.

Wani mazaunin da ke zaune a kusa da kasuwar ya ce, daukin gaggawa da jami’an kashe gobara suka yi ne ya ceci kasuwar daga barnar gaba daya.

Majiyar wadda ba ta fayyace musabbabin gobarar ba, ta ce kasuwar na da saurin barkewar gobara a duk shekara.

Hukumar kashe gobara ta jihar ba ta ce uffan ba kan lamarin, sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Suleiman Nguroje ya ce an shawo kan lamarin.

Ya bayyana cewa nan take rundunar ‘yan sandan jihar ta samu rahoton barkewar gobarar, kwamishinan ‘yan sandan, CP Afolabi Babatola, ya tura karin jami,ai domin hana ’yan bata gari yin fashi a cikin kasuwar.
“Tare da goyon bayan ‘yan kwana-kwana, an shawo kan lamarin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp