Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan jihar Adamawa ta tabbatar da aukuwar gobara a kasuwar...

Rundunar ‘Yan Sandan jihar Adamawa ta tabbatar da aukuwar gobara a kasuwar Yola

Gobara ta lalata wasu sassan babbar kasuwar garin Yola.

Rahotannin sun bayyana cewa go barar ta tashi ne  a daren Litinin yayin da yan kasuwar ke a rufe.

Wasu majiyoyi da dama sun ce shaguna da dama ne lamarin ya shafa, sannan gobarar ta yi sanadayar a sarar kayayyakin miliyoyin Naira.

Wani mazaunin da ke zaune a kusa da kasuwar ya ce, daukin gaggawa da jami’an kashe gobara suka yi ne ya ceci kasuwar daga barnar gaba daya.

Majiyar wadda ba ta fayyace musabbabin gobarar ba, ta ce kasuwar na da saurin barkewar gobara a duk shekara.

Hukumar kashe gobara ta jihar ba ta ce uffan ba kan lamarin, sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Suleiman Nguroje ya ce an shawo kan lamarin.

Ya bayyana cewa nan take rundunar ‘yan sandan jihar ta samu rahoton barkewar gobarar, kwamishinan ‘yan sandan, CP Afolabi Babatola, ya tura karin jami,ai domin hana ’yan bata gari yin fashi a cikin kasuwar.
“Tare da goyon bayan ‘yan kwana-kwana, an shawo kan lamarin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp