Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan jihar Adamawa ta tabbatar da aukuwar gobara a kasuwar...

Rundunar ‘Yan Sandan jihar Adamawa ta tabbatar da aukuwar gobara a kasuwar Yola

Gobara ta lalata wasu sassan babbar kasuwar garin Yola.

Rahotannin sun bayyana cewa go barar ta tashi ne  a daren Litinin yayin da yan kasuwar ke a rufe.

Wasu majiyoyi da dama sun ce shaguna da dama ne lamarin ya shafa, sannan gobarar ta yi sanadayar a sarar kayayyakin miliyoyin Naira.

Wani mazaunin da ke zaune a kusa da kasuwar ya ce, daukin gaggawa da jami’an kashe gobara suka yi ne ya ceci kasuwar daga barnar gaba daya.

Majiyar wadda ba ta fayyace musabbabin gobarar ba, ta ce kasuwar na da saurin barkewar gobara a duk shekara.

Hukumar kashe gobara ta jihar ba ta ce uffan ba kan lamarin, sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Suleiman Nguroje ya ce an shawo kan lamarin.

Ya bayyana cewa nan take rundunar ‘yan sandan jihar ta samu rahoton barkewar gobarar, kwamishinan ‘yan sandan, CP Afolabi Babatola, ya tura karin jami,ai domin hana ’yan bata gari yin fashi a cikin kasuwar.
“Tare da goyon bayan ‘yan kwana-kwana, an shawo kan lamarin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp