Home Labarai Gwamnan jihar Jigawa ya kori shugaban asibitin Gumel

Gwamnan jihar Jigawa ya kori shugaban asibitin Gumel

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ya amince da hukuncin ladabtarwa ga jagororin Babban Asibitin Gumel da ke Jihar Jigawa.

Wannan na zuwa ne bayan ziyarar bazata da gwamnan ya kai Babban Asibitin a ranar Juma’ar da ta gabata, inda ya tarar da asibitin cikin mummunan yanayi da kuma rashin bayar da kulawar lafiya ga majinyata yanda ya kamata.

Sanarwar da Mai Magana da Yawun Gwamnan, Hamisu Gumel ya sanyawa hannu, ta ce, Gwamnan ya rushe Hukumar Gudanarwar asibitin tare da ɗauke manyan jami’an asibitin inda aka mayar da su Ma’aikatar Lafiya da ke Dutse domin su jira hukuncin da ya dace da su bayan an kammala bincike.

Jami’an da abun ya shafa sun haɗa da Shugaban Asibitin, Daraktan Kula Bayar da Duba Marassa Lafiya, Daraktan Mulki, Shugaban Sashin Bayar da Magani, Shugaban Sashin Gwaje-gwaje da kuma Mai Kula da Hada-hadar Kuɗi na asibitin.

Cikin laifukan da Gwamna Namadi ya kama ana aikatawa a asibitin akwai, tursasawa marassa lafiya biyan naira 7000 domin a ɗau jinin ƴan’uwansu a ƙarawa majinyatansu, tursasawa majinyata siyan auduga, rashin samar da ruwan famfo duk da gwamnati ta bayar da kuɗin yin hakan, da kuma rashin zuwa aiki a ɓangaren shugabannin asibitin na Gumel.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp