Home Labarai Gwamnan jihar Jigawa ya kori shugaban asibitin Gumel

Gwamnan jihar Jigawa ya kori shugaban asibitin Gumel

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ya amince da hukuncin ladabtarwa ga jagororin Babban Asibitin Gumel da ke Jihar Jigawa.

Wannan na zuwa ne bayan ziyarar bazata da gwamnan ya kai Babban Asibitin a ranar Juma’ar da ta gabata, inda ya tarar da asibitin cikin mummunan yanayi da kuma rashin bayar da kulawar lafiya ga majinyata yanda ya kamata.

Sanarwar da Mai Magana da Yawun Gwamnan, Hamisu Gumel ya sanyawa hannu, ta ce, Gwamnan ya rushe Hukumar Gudanarwar asibitin tare da ɗauke manyan jami’an asibitin inda aka mayar da su Ma’aikatar Lafiya da ke Dutse domin su jira hukuncin da ya dace da su bayan an kammala bincike.

Jami’an da abun ya shafa sun haɗa da Shugaban Asibitin, Daraktan Kula Bayar da Duba Marassa Lafiya, Daraktan Mulki, Shugaban Sashin Bayar da Magani, Shugaban Sashin Gwaje-gwaje da kuma Mai Kula da Hada-hadar Kuɗi na asibitin.

Cikin laifukan da Gwamna Namadi ya kama ana aikatawa a asibitin akwai, tursasawa marassa lafiya biyan naira 7000 domin a ɗau jinin ƴan’uwansu a ƙarawa majinyatansu, tursasawa majinyata siyan auduga, rashin samar da ruwan famfo duk da gwamnati ta bayar da kuɗin yin hakan, da kuma rashin zuwa aiki a ɓangaren shugabannin asibitin na Gumel.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp