Home Labarai Gwamnan jihar Jigawa ya kori shugaban asibitin Gumel

Gwamnan jihar Jigawa ya kori shugaban asibitin Gumel

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ya amince da hukuncin ladabtarwa ga jagororin Babban Asibitin Gumel da ke Jihar Jigawa.

Wannan na zuwa ne bayan ziyarar bazata da gwamnan ya kai Babban Asibitin a ranar Juma’ar da ta gabata, inda ya tarar da asibitin cikin mummunan yanayi da kuma rashin bayar da kulawar lafiya ga majinyata yanda ya kamata.

Sanarwar da Mai Magana da Yawun Gwamnan, Hamisu Gumel ya sanyawa hannu, ta ce, Gwamnan ya rushe Hukumar Gudanarwar asibitin tare da ɗauke manyan jami’an asibitin inda aka mayar da su Ma’aikatar Lafiya da ke Dutse domin su jira hukuncin da ya dace da su bayan an kammala bincike.

Jami’an da abun ya shafa sun haɗa da Shugaban Asibitin, Daraktan Kula Bayar da Duba Marassa Lafiya, Daraktan Mulki, Shugaban Sashin Bayar da Magani, Shugaban Sashin Gwaje-gwaje da kuma Mai Kula da Hada-hadar Kuɗi na asibitin.

Cikin laifukan da Gwamna Namadi ya kama ana aikatawa a asibitin akwai, tursasawa marassa lafiya biyan naira 7000 domin a ɗau jinin ƴan’uwansu a ƙarawa majinyatansu, tursasawa majinyata siyan auduga, rashin samar da ruwan famfo duk da gwamnati ta bayar da kuɗin yin hakan, da kuma rashin zuwa aiki a ɓangaren shugabannin asibitin na Gumel.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp