Home Labarai Tinubu ya kaddamar da matakan inganta tattalin arzikin

Tinubu ya kaddamar da matakan inganta tattalin arzikin

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana kaddamar da wasu matakai daban daban da za su zaburar da tattalin arzikin kasar da zummar shawo kan kuncin rayuwar da jama’ar kasar suka shiga sakamakon cire tallafin man fetur.

‘yan tsiraru kawai ke amfana da shi, yayin da akasarin jama’ar kasar ke shan wahala.

Shugaban ya ce a cikin watanni biyu da suka yi a karagar mulki, gwamnatin sa ta yi nasarar ceto sama da naira triliyan guda daga cikin makudan kudaden da ake zubawa a matsayin tallafin man, wadanda za’a karkatu su wajen bunkasa harkar ilimi da harkokin kula da lafiya da kuma samar da kayan more rayuwa.

Tinubu wanda ya ce ya fahimci halin kuncin da ‘yan Najeriya suke ciki, ya kuma bayyana shirye shirye da dama da gwamnatin sa za ta aiwatar wajen samar da rance ga masu kanana da matsakaitan masana’antu domin bunkasa harkokin su ta yadda za su amfana ta hanyar biyan kashi 9 na kudin ruwa.

Shugaban ya kuma jinjinawa masu kamfanoni da masana’antu saboda dagewar da su ke da ita wajen ci gaba da harkokin su a cikin irin wannan yanayi mai tsauri.

Shugaban Najeriyar Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatin sa na tattaunawa da kungiyoyin kwadago da zummar kara albashin ma’aikata saboda tinkarar halin da ake ciki, yayin da kuma ya ce zai aiwatar da shirin sa da ya yi alkawari na tallafawa marasa karfi a cikin al’umma

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp