Home Labarai Tinubu ya kaddamar da matakan inganta tattalin arzikin

Tinubu ya kaddamar da matakan inganta tattalin arzikin

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana kaddamar da wasu matakai daban daban da za su zaburar da tattalin arzikin kasar da zummar shawo kan kuncin rayuwar da jama’ar kasar suka shiga sakamakon cire tallafin man fetur.

‘yan tsiraru kawai ke amfana da shi, yayin da akasarin jama’ar kasar ke shan wahala.

Shugaban ya ce a cikin watanni biyu da suka yi a karagar mulki, gwamnatin sa ta yi nasarar ceto sama da naira triliyan guda daga cikin makudan kudaden da ake zubawa a matsayin tallafin man, wadanda za’a karkatu su wajen bunkasa harkar ilimi da harkokin kula da lafiya da kuma samar da kayan more rayuwa.

Tinubu wanda ya ce ya fahimci halin kuncin da ‘yan Najeriya suke ciki, ya kuma bayyana shirye shirye da dama da gwamnatin sa za ta aiwatar wajen samar da rance ga masu kanana da matsakaitan masana’antu domin bunkasa harkokin su ta yadda za su amfana ta hanyar biyan kashi 9 na kudin ruwa.

Shugaban ya kuma jinjinawa masu kamfanoni da masana’antu saboda dagewar da su ke da ita wajen ci gaba da harkokin su a cikin irin wannan yanayi mai tsauri.

Shugaban Najeriyar Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatin sa na tattaunawa da kungiyoyin kwadago da zummar kara albashin ma’aikata saboda tinkarar halin da ake ciki, yayin da kuma ya ce zai aiwatar da shirin sa da ya yi alkawari na tallafawa marasa karfi a cikin al’umma

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp