Home DUNIYA RFI da France 24 sun yi tur da rufe tashoshinsu a Nijar

RFI da France 24 sun yi tur da rufe tashoshinsu a Nijar

Gidan rediyon RFI da gidan talabijin na France 24 sun yi Allah-wadai da matakin da hukumomin sojin Nijar suka dauka na dakatar da su daga yada shirye-shiryensu a kasar, mako guda da juyin mulkin da sojojin suka yi a kasar.

Hukumar Gudanarwa kafofin yada Faransa a kasashen ketare ta France Medias Monde ta bayyana matakin a matsayin wanda ya yi hannun riga da dokokin shari’a, lamarin da ta ce zai dakile wa ‘yan kasar hanyoyin da suke samun cikakkun labarai cikin ‘yanci.

Wannan na zuwa ne bayan irin wannan dakatarwar da sojojin da ke mulki a Mali da Burkina Faso suka yi wa RFI da France 24 a watannin da suka shude.

Hukumar ta France Medias Monde ta jaddada kudirinta ga ‘yancin yada labarai da kuma kare lafiyar ‘yan jaridarta.

RFI na yada shirye-shiryensa a tashoshin FM guda bakwai baya ga gajeren zango da sauran hanyoyin tauraron dan adam cikin harsunan Faransanci da Hausa da Fulfulde.

Kazalika akwai wasu karin gidajen rediyo 44, abokan huldar RFI da su ma ke yada shirye-shiryensa cikin harsunan Faransanci da Hausa da Fulfulde a Nijar.

A shekarar 2022, wasu alkaluma da aka tattara sun nuna cewa, kimanin masu saurare miliyan 1 da dubu 900 ne ke sauraren RFI a kowanne mako a kasar ta Nijar, wato kwatankwacin kashi 18 na daukacin al’ummar kasar, yayin da RFI din ke zama kafar yada labarai ta ketare mafi girma a kasar kamar yadda wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a ta nuna.

Har ila yau, alkaluman sun nuna cewa, kimanin rubu’in daukacin jama’ar Nijar ne suka bibiyar tashar ta RFI a kowanne mako a shekarar bara.

Koda yake har yanzu ana iya samun RFI da France 24 ta hanyoyin tauraron dan adam kai tsaye kamar su Eutelsat da Arab-Sat, sai kuma gajeren zango.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp