Home DUNIYA RFI da France 24 sun yi tur da rufe tashoshinsu a Nijar

RFI da France 24 sun yi tur da rufe tashoshinsu a Nijar

Gidan rediyon RFI da gidan talabijin na France 24 sun yi Allah-wadai da matakin da hukumomin sojin Nijar suka dauka na dakatar da su daga yada shirye-shiryensu a kasar, mako guda da juyin mulkin da sojojin suka yi a kasar.

Hukumar Gudanarwa kafofin yada Faransa a kasashen ketare ta France Medias Monde ta bayyana matakin a matsayin wanda ya yi hannun riga da dokokin shari’a, lamarin da ta ce zai dakile wa ‘yan kasar hanyoyin da suke samun cikakkun labarai cikin ‘yanci.

Wannan na zuwa ne bayan irin wannan dakatarwar da sojojin da ke mulki a Mali da Burkina Faso suka yi wa RFI da France 24 a watannin da suka shude.

Hukumar ta France Medias Monde ta jaddada kudirinta ga ‘yancin yada labarai da kuma kare lafiyar ‘yan jaridarta.

RFI na yada shirye-shiryensa a tashoshin FM guda bakwai baya ga gajeren zango da sauran hanyoyin tauraron dan adam cikin harsunan Faransanci da Hausa da Fulfulde.

Kazalika akwai wasu karin gidajen rediyo 44, abokan huldar RFI da su ma ke yada shirye-shiryensa cikin harsunan Faransanci da Hausa da Fulfulde a Nijar.

A shekarar 2022, wasu alkaluma da aka tattara sun nuna cewa, kimanin masu saurare miliyan 1 da dubu 900 ne ke sauraren RFI a kowanne mako a kasar ta Nijar, wato kwatankwacin kashi 18 na daukacin al’ummar kasar, yayin da RFI din ke zama kafar yada labarai ta ketare mafi girma a kasar kamar yadda wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a ta nuna.

Har ila yau, alkaluman sun nuna cewa, kimanin rubu’in daukacin jama’ar Nijar ne suka bibiyar tashar ta RFI a kowanne mako a shekarar bara.

Koda yake har yanzu ana iya samun RFI da France 24 ta hanyoyin tauraron dan adam kai tsaye kamar su Eutelsat da Arab-Sat, sai kuma gajeren zango.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp