Home Labarai Rundunar ƴan sandan jahar Kano ta cafke mutane 62 da ake zargi...

Rundunar ƴan sandan jahar Kano ta cafke mutane 62 da ake zargi da aikata laifukan fashi da Makami a jihar

Rundunar ƴan sandan jahar Kano ta cafke mutane 62 da ake zargi da aikata laifukan fashi da Makami, Sata da aikata Daba da kuma Dilolin ƙwaya da dai sauransu.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne, ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar juma’a .

Sanarwar ta ce, an samu nasarar ƙwato muggan makamai guda 46 , sai codeine 253 , madarar Sukudayin 200 da kuma ƙulli-ƙulli na tabar wawi guda 1,802 da Babura biyu sa sauran muggan ƙwayoyi.

Kwamishinan ƴan sandan jahar Kano CP Muhammad Usaini Gumel ya godewa al’ummar jahar bisa haɗin kai da goyon bayan sa suke bawa rundunar a koda yaushe.

Kiyawa ya ƙara da cewa, nasarar ra biyo bayan miƙa wuya da wasu matasa 99 suka yi sa ake zargi da aiyukan Faɗan Fada a cikin birnin Kano, waɗanda suka Tuba tare da ajiye makamansu.

Rundunar ƴan sandan jahar ta sanya tukwicin Naira dubu ɗari 300,000. ga dukkan wanda ya bauyar da bayanan sirri kan wasu matasa uku da suka ƙi miƙa wuya dan a cafke su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp