Home DUNIYA Gwamnatin Habasha ta saka dokar ta baci ta tsahon watanni 6

Gwamnatin Habasha ta saka dokar ta baci ta tsahon watanni 6

Gwamantin habasha ta saka dokar ta baci ta watanni shidda a yankin Amhara, yanki na biyu mafi gima a kasar.

Wannan na zuwa ne biyo bayan wasu arangama da ake tsakanin dakarun sojin kasar da wasu gungun mayaka, abinda ya haifar da dakatar da zirga-zirga.

Rikicin daya barke a yanki a wannan mako, ya zama babbar barazana ga tsaron kasar shekaru biyu bayan rikicin yankin Tigray wadda ke makotaka da Amhara.

Gwamantin yankin Amhara ta bukaci tallafin Karin jami’an tsaro daga gwamantin tarayyar kasar domin tabbatar da zaman lafiya.

Ta cikin wata sanarwa da ofishin friminista kasar Abiy Ahmad ya fitar yace, ya zame mana wajibi mu Sanya dokar ta bacin domin samar da tsaro kafin lamarin ya ta’azzara.

Habasha ce kasa ta biyu mafi yawan al’umma bayan Nijeriya, na fuskantar matsalar tashe-tashen hankula, tun bayan darewar Abiy Ahmad karagar mulkin kasar a shekarar 2018, duk da cewa ya sami lambar yabo ta zaman lafiya a shekarar 2019 bisa gudunmawar daya bayar wajen samar da zaman lafiya a kasar Eritrea.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp