Home DUNIYA Gwamnatin Habasha ta saka dokar ta baci ta tsahon watanni 6

Gwamnatin Habasha ta saka dokar ta baci ta tsahon watanni 6

Gwamantin habasha ta saka dokar ta baci ta watanni shidda a yankin Amhara, yanki na biyu mafi gima a kasar.

Wannan na zuwa ne biyo bayan wasu arangama da ake tsakanin dakarun sojin kasar da wasu gungun mayaka, abinda ya haifar da dakatar da zirga-zirga.

Rikicin daya barke a yanki a wannan mako, ya zama babbar barazana ga tsaron kasar shekaru biyu bayan rikicin yankin Tigray wadda ke makotaka da Amhara.

Gwamantin yankin Amhara ta bukaci tallafin Karin jami’an tsaro daga gwamantin tarayyar kasar domin tabbatar da zaman lafiya.

Ta cikin wata sanarwa da ofishin friminista kasar Abiy Ahmad ya fitar yace, ya zame mana wajibi mu Sanya dokar ta bacin domin samar da tsaro kafin lamarin ya ta’azzara.

Habasha ce kasa ta biyu mafi yawan al’umma bayan Nijeriya, na fuskantar matsalar tashe-tashen hankula, tun bayan darewar Abiy Ahmad karagar mulkin kasar a shekarar 2018, duk da cewa ya sami lambar yabo ta zaman lafiya a shekarar 2019 bisa gudunmawar daya bayar wajen samar da zaman lafiya a kasar Eritrea.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp