Home DUNIYA Gwamnatin Habasha ta saka dokar ta baci ta tsahon watanni 6

Gwamnatin Habasha ta saka dokar ta baci ta tsahon watanni 6

Gwamantin habasha ta saka dokar ta baci ta watanni shidda a yankin Amhara, yanki na biyu mafi gima a kasar.

Wannan na zuwa ne biyo bayan wasu arangama da ake tsakanin dakarun sojin kasar da wasu gungun mayaka, abinda ya haifar da dakatar da zirga-zirga.

Rikicin daya barke a yanki a wannan mako, ya zama babbar barazana ga tsaron kasar shekaru biyu bayan rikicin yankin Tigray wadda ke makotaka da Amhara.

Gwamantin yankin Amhara ta bukaci tallafin Karin jami’an tsaro daga gwamantin tarayyar kasar domin tabbatar da zaman lafiya.

Ta cikin wata sanarwa da ofishin friminista kasar Abiy Ahmad ya fitar yace, ya zame mana wajibi mu Sanya dokar ta bacin domin samar da tsaro kafin lamarin ya ta’azzara.

Habasha ce kasa ta biyu mafi yawan al’umma bayan Nijeriya, na fuskantar matsalar tashe-tashen hankula, tun bayan darewar Abiy Ahmad karagar mulkin kasar a shekarar 2018, duk da cewa ya sami lambar yabo ta zaman lafiya a shekarar 2019 bisa gudunmawar daya bayar wajen samar da zaman lafiya a kasar Eritrea.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp