Home DUNIYA Sojojin ECOWAS sun kagu su kaddamar da Matakin soji kan Jamhuriyar Nijar

Sojojin ECOWAS sun kagu su kaddamar da Matakin soji kan Jamhuriyar Nijar

Ƙasashen Yammacin Afrika sun amince da wani tsari na ɗaukar matakin soji kan Nijar, idan har sojojin da suka yi juyin mulki suka ƙi amincewa da sharaɗin dawo da hamɓarren shugaba, Mohamed Bazoum bisa karagar mulkin.

Tun da farko ECOWAS ta bai wa sojojin na jamhuriyar Nijar wa’adin ranar Lahadi su mayar da mulki ga farar hula.

Alamu na nuna cewa sojojin Ecowas sun ƙagu da su ƙaddamar da yaƙi a Nijar idan har hakan ya zama dole.

Yanzu haka dai, Najeriya ta rufe iyakokin ƙasar da Nijar, ta kuma yanke wutar da take bai wa Nijar din duk a lokaci guda, matakan sun haddasa tashin farashin kayan masarufi a ƙasar, hakan na nuna yadda matakan Ecowas ɗin za su haddasa wahalhalu ga ƴan ƙasar.

A ranar Alhamis wata tawaga ta kungiyar ta je Nijar, domin shiga tsakani sai dai ba ta samu damar ganawa da shugaban mulkin sojin ba, da ma hamɓararren shugaban na farar hula.

Masu aiko da rahotanni sun ce, ɗaukar matakin soji kan lamarin zai iya zama mai wahala sosai, saboda kayan aiki, da kuma hadari, domin zai iya kara dagula al’amura a yankin, wanda masu ikirarin jihadi ke yi wa ta’annati.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp