Home DUNIYA Su Kawo Sumaila sun yi fatali da bukatar Tinubu Kan Jamhuriyar Nijar

Su Kawo Sumaila sun yi fatali da bukatar Tinubu Kan Jamhuriyar Nijar

Yan majalisar dattawa da suka Fito daga Yankin arewacin Nijeriya sun kalubalanci yunkurin kungiyar raya tattalin arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS, na amfani da karfin soji kan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar.

Sun bayyana haka ne a yayin da shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya rubuta wasika ga majalisar dattawan kasar yana neman amincewarta don daukar matakin soji kan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar.

Shugaban ya kuma nemi izinin daukar wasu matakai ciki har da katse wutar lantarkin da Nijeriya ke bai wa Nijar.

Mai Magana Da Yawun Kungiyar Kuma Sanatan Kano ta kudu Sanata Abdurrahman kawu sumaila yace Baza su amince da duk wani Mataki na yaki da Nijeriya da Jamhuriyar Niger ba, Saboda doguwar alakar Dake tsakanin Yankin arewacin Nigeria da ita.

Shugaban majalisar dattawan kasar Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar da Shugaba Tinubu ya rubuta wa majalisar a zaman da ta yi ranar Juma’a.

Ya aike da wasikar ne bayan rashin nasarar tawagar da kungiyar ECOWAS ta tura Nijar don tattaunawa da sojojin kasar don mayar da Shugaba Mohamed Bazoum kan karagar mulki.

Tuni dai sojojin ECOWAS suka fara nuna bukatar su na afkawa dakarun sojin na Nijar domin dawo da Kasar turbar Damukradiyya.

PRNigeria Nijeriya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp