Home DUNIYA Su Kawo Sumaila sun yi fatali da bukatar Tinubu Kan Jamhuriyar Nijar

Su Kawo Sumaila sun yi fatali da bukatar Tinubu Kan Jamhuriyar Nijar

Yan majalisar dattawa da suka Fito daga Yankin arewacin Nijeriya sun kalubalanci yunkurin kungiyar raya tattalin arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS, na amfani da karfin soji kan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar.

Sun bayyana haka ne a yayin da shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya rubuta wasika ga majalisar dattawan kasar yana neman amincewarta don daukar matakin soji kan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar.

Shugaban ya kuma nemi izinin daukar wasu matakai ciki har da katse wutar lantarkin da Nijeriya ke bai wa Nijar.

Mai Magana Da Yawun Kungiyar Kuma Sanatan Kano ta kudu Sanata Abdurrahman kawu sumaila yace Baza su amince da duk wani Mataki na yaki da Nijeriya da Jamhuriyar Niger ba, Saboda doguwar alakar Dake tsakanin Yankin arewacin Nigeria da ita.

Shugaban majalisar dattawan kasar Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar da Shugaba Tinubu ya rubuta wa majalisar a zaman da ta yi ranar Juma’a.

Ya aike da wasikar ne bayan rashin nasarar tawagar da kungiyar ECOWAS ta tura Nijar don tattaunawa da sojojin kasar don mayar da Shugaba Mohamed Bazoum kan karagar mulki.

Tuni dai sojojin ECOWAS suka fara nuna bukatar su na afkawa dakarun sojin na Nijar domin dawo da Kasar turbar Damukradiyya.

PRNigeria Nijeriya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp