Home DUNIYA Amurka za ta ci gaba da bai wa Nijar tallafin Abinci

Amurka za ta ci gaba da bai wa Nijar tallafin Abinci

Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya ce Amurka za ta ci gaba da bayar da taimakon kayan agaji da tallafin abinci ga Jamhuriyar Nijar.

To sai dai Mista Blinken ya ce Amurka za ta dakatar da wasu tallafin da za su taimaka wa ƙasar da ke yammacin Afirka.

Ya ce Amurka za ta ci gaba da samar da tsaro don kare jami’anta da ke ƙasar.

Kalaman Mista Blinken na zuwa ne a daidai lokacin ƙasashen ƙungiyar Ecowas suka amince da amfani da ƙarfin soji a Nijar ɗin, matuƙar sojojin ba su mayar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Mohamed Bazoum kan mulki ba.

Tuni dai Nijar din ta sanar da janye jakadunta da ke wasu ƙasashen duniya ciki har da Amurka da faransa da kuma Najeriya.

A ranar Juma’a ne dai Najeriya ta sanar da rufe kan iyakokin ƙasar da Jamhuriyar ta Nijar, bayan katse wutar lantarki da take bai wa ƙasar, a wani mataki na tilasta wa sojojin mayar da Bazoum kan mulki.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp