Home DUNIYA Amurka za ta ci gaba da bai wa Nijar tallafin Abinci

Amurka za ta ci gaba da bai wa Nijar tallafin Abinci

Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya ce Amurka za ta ci gaba da bayar da taimakon kayan agaji da tallafin abinci ga Jamhuriyar Nijar.

To sai dai Mista Blinken ya ce Amurka za ta dakatar da wasu tallafin da za su taimaka wa ƙasar da ke yammacin Afirka.

Ya ce Amurka za ta ci gaba da samar da tsaro don kare jami’anta da ke ƙasar.

Kalaman Mista Blinken na zuwa ne a daidai lokacin ƙasashen ƙungiyar Ecowas suka amince da amfani da ƙarfin soji a Nijar ɗin, matuƙar sojojin ba su mayar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Mohamed Bazoum kan mulki ba.

Tuni dai Nijar din ta sanar da janye jakadunta da ke wasu ƙasashen duniya ciki har da Amurka da faransa da kuma Najeriya.

A ranar Juma’a ne dai Najeriya ta sanar da rufe kan iyakokin ƙasar da Jamhuriyar ta Nijar, bayan katse wutar lantarki da take bai wa ƙasar, a wani mataki na tilasta wa sojojin mayar da Bazoum kan mulki.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp