Home Labarai Tinubu ya sanar da Majalisar Dokoki aniyar tura dakaru zuwa Nijar

Tinubu ya sanar da Majalisar Dokoki aniyar tura dakaru zuwa Nijar

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya shaida wa majalisar dokokin Najeriya matsayar da ƙungiyar Ecowas ta cimma kan ɗaukar matakin soji a kan Nijar da kuma sauran takunkuman da aka ɗauka na ladabtar da sojojin da suka yi juyin mulki.

Shugaban majalisar dattawan Najeriya, Godswill Akpabio ya sanar da saƙon shugaban ƙasar inda ya karanto kai tsaye daga wasikar shugaba Tinubun.

Wasikar na cewa “Bayan abin takaicin da ya faru a Nijar inda aka hamɓarar da shugaban ƙasa, Ecowas a ƙarƙashin jagorancina ta yi Allah-wadai da juyin mulkin kuma ta amince da ɗaukar matakan dawo da Nijar kan turbar dimokuraɗiyya. A wani mataki na dawo da zaman lafiya a ƙasar Ecowas ta fitar da matsaya.

“Za a rufe duk iyakokin Nijar da ƙasashenmu da kuma sanya ido don tabbatar da cewa an yi biyayya ga matakin.

“Yanke wutar lantarkin da ake kaiwa Nijar da neman goyon bayan ƙasashen duniya wajen aiwatar da matsayar ƙungiyar Ecowas da kuma datse sufurin jirgin sama daga cikin Nijar da ma wanda zai shiga ƙasar.

“Rufe hanyoyin shigar da kaya Nijar daga Legas da kuma wayar da kan ƴan Najeriya musamman a kafafen sada zumunta game da shirin ɗaukar matakin soji a kan sojojin Nijar ɗin.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp