Home Labarai Tinubu ya sanar da Majalisar Dokoki aniyar tura dakaru zuwa Nijar

Tinubu ya sanar da Majalisar Dokoki aniyar tura dakaru zuwa Nijar

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya shaida wa majalisar dokokin Najeriya matsayar da ƙungiyar Ecowas ta cimma kan ɗaukar matakin soji a kan Nijar da kuma sauran takunkuman da aka ɗauka na ladabtar da sojojin da suka yi juyin mulki.

Shugaban majalisar dattawan Najeriya, Godswill Akpabio ya sanar da saƙon shugaban ƙasar inda ya karanto kai tsaye daga wasikar shugaba Tinubun.

Wasikar na cewa “Bayan abin takaicin da ya faru a Nijar inda aka hamɓarar da shugaban ƙasa, Ecowas a ƙarƙashin jagorancina ta yi Allah-wadai da juyin mulkin kuma ta amince da ɗaukar matakan dawo da Nijar kan turbar dimokuraɗiyya. A wani mataki na dawo da zaman lafiya a ƙasar Ecowas ta fitar da matsaya.

“Za a rufe duk iyakokin Nijar da ƙasashenmu da kuma sanya ido don tabbatar da cewa an yi biyayya ga matakin.

“Yanke wutar lantarkin da ake kaiwa Nijar da neman goyon bayan ƙasashen duniya wajen aiwatar da matsayar ƙungiyar Ecowas da kuma datse sufurin jirgin sama daga cikin Nijar da ma wanda zai shiga ƙasar.

“Rufe hanyoyin shigar da kaya Nijar daga Legas da kuma wayar da kan ƴan Najeriya musamman a kafafen sada zumunta game da shirin ɗaukar matakin soji a kan sojojin Nijar ɗin.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp