Kotu ta kwace zaman Dan majalisa a jihar Kano

Kotun sauraron ƙorafin zaɓe da ke zama a Kano ta soke zaɓen Honourable Muktar Umar Yarima mai wakiltar Tarauni a majalisar wakilai saboda amfani da takardu shaidar kammala karatu na bogi.

A hukuncin da alƙalan kotun uku suka bayar, sun ce sun samu Yarima da gabatar da takardar kammala karatun firamare na bogi, don haka kotun ta umarci hukumar zabe ta ƙasa ta ayyana ɗan takarar jam’iyyar APC, Honourable Hafizu Ibrahim Kawu a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

A baya dai jami’in sanar da sakamakon zaben mazabar Tarauni, a zaɓen da ya gabata, Garba Galadanci ya sanar da Yarima na jam’iyyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben, bayan samun ƙuri’a 26,273, ya kuma doke Honourable Hafizu Ibrahim Kawu na jam’iyyar APC wanda ya samu ƙuri’a 15,931.

Daga baya Kawu ya shigar da ƙara, inda ya ƙalubalanci sakamakon zaɓen a bisa zargin gabatar da takardun bogi daga ɓangaren wanda ya yi nasarar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1187 days 17 hours 48 minutes 35 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1169 days 19 hours 30 minutes 0 second

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com