Home Labarai Gwamnatin tarayya Nijeriya ta kafa kwamitin kan harkar tara haraji

Gwamnatin tarayya Nijeriya ta kafa kwamitin kan harkar tara haraji

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ƙaddamar da wani kwamiti da zai yi garambawul a harkar tara haraji da manufofin kuɗi, a yunƙurinsa na ganin haraji ya zama kashi 18% na arziƙin da Najeriya ke samu cikin duk abin da ta sarrafa a gida, wato GDP, nan da shekara uku.

Shugaban ya ce matakin zai taimaka wajen ganin Najeriya ta rage dogaro a kan bashi wajen samun kuɗin gudanar da harkokin gwamnati.

Wata sanarwa da mashawarcin shugaban Najeriyar na musamman kan harkar yaɗa labarai, Ajuri Ngelale, ya fitar ta ambato Tinubu na umartar shugaban kwamitin, Taiwo Oyedele, ya yi nazari don gyaran fuska a harkokin kuɗi da garambawul a harkar tara haraji da kuma kyautata bunƙasar tattalin arziƙi a cikin shekara ɗaya.

Tinubu ya ce Najeriya har yanzu tana fuskantar ƙalubale a ɓangarorin da suka haɗar da biyan haraji cikin sauƙi, kuma kason haraji da take karɓa idan an kwatanta da kuɗin da take samu daga duk abin da ta sarrafa a gida ya yi kaɗan. A cewarsa ƙasar, ta zama kurar baya a Afirka a wannan ɓangare.

Sanarwar ta ce manufar shugaban ƙasar ita ce yi wa tsarin karɓar haraji gyaran fuska don tallafa wa bunƙasa harkokin ci gaba mai ɗorewa.

Ya ce matuƙar babu kuɗin shiga, gwamnati ba za ta iya samar isassun ayyukan inganta rayuwa ga al’ummar da suka ba ta amana ba.

Shugaba Tinubu ya ba da umarnin cewa ana sa ran kwamitin zai gabatar da wani tsarin garambawul cikin gaggawa da za a iya aiwatarwa a cikin kwana 30. Sai kuma ba da shawarwari kan muhimman sauye-sauye a cikin wata shida, aiwatar da cikakkun tsare-tsaren a cikin shekara ɗaya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp