Home Labarai Gwamnatin tarayya Nijeriya ta kafa kwamitin kan harkar tara haraji

Gwamnatin tarayya Nijeriya ta kafa kwamitin kan harkar tara haraji

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ƙaddamar da wani kwamiti da zai yi garambawul a harkar tara haraji da manufofin kuɗi, a yunƙurinsa na ganin haraji ya zama kashi 18% na arziƙin da Najeriya ke samu cikin duk abin da ta sarrafa a gida, wato GDP, nan da shekara uku.

Shugaban ya ce matakin zai taimaka wajen ganin Najeriya ta rage dogaro a kan bashi wajen samun kuɗin gudanar da harkokin gwamnati.

Wata sanarwa da mashawarcin shugaban Najeriyar na musamman kan harkar yaɗa labarai, Ajuri Ngelale, ya fitar ta ambato Tinubu na umartar shugaban kwamitin, Taiwo Oyedele, ya yi nazari don gyaran fuska a harkokin kuɗi da garambawul a harkar tara haraji da kuma kyautata bunƙasar tattalin arziƙi a cikin shekara ɗaya.

Tinubu ya ce Najeriya har yanzu tana fuskantar ƙalubale a ɓangarorin da suka haɗar da biyan haraji cikin sauƙi, kuma kason haraji da take karɓa idan an kwatanta da kuɗin da take samu daga duk abin da ta sarrafa a gida ya yi kaɗan. A cewarsa ƙasar, ta zama kurar baya a Afirka a wannan ɓangare.

Sanarwar ta ce manufar shugaban ƙasar ita ce yi wa tsarin karɓar haraji gyaran fuska don tallafa wa bunƙasa harkokin ci gaba mai ɗorewa.

Ya ce matuƙar babu kuɗin shiga, gwamnati ba za ta iya samar isassun ayyukan inganta rayuwa ga al’ummar da suka ba ta amana ba.

Shugaba Tinubu ya ba da umarnin cewa ana sa ran kwamitin zai gabatar da wani tsarin garambawul cikin gaggawa da za a iya aiwatarwa a cikin kwana 30. Sai kuma ba da shawarwari kan muhimman sauye-sauye a cikin wata shida, aiwatar da cikakkun tsare-tsaren a cikin shekara ɗaya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp