Home Labarai Gwamnatin tarayya Nijeriya ta kafa kwamitin kan harkar tara haraji

Gwamnatin tarayya Nijeriya ta kafa kwamitin kan harkar tara haraji

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ƙaddamar da wani kwamiti da zai yi garambawul a harkar tara haraji da manufofin kuɗi, a yunƙurinsa na ganin haraji ya zama kashi 18% na arziƙin da Najeriya ke samu cikin duk abin da ta sarrafa a gida, wato GDP, nan da shekara uku.

Shugaban ya ce matakin zai taimaka wajen ganin Najeriya ta rage dogaro a kan bashi wajen samun kuɗin gudanar da harkokin gwamnati.

Wata sanarwa da mashawarcin shugaban Najeriyar na musamman kan harkar yaɗa labarai, Ajuri Ngelale, ya fitar ta ambato Tinubu na umartar shugaban kwamitin, Taiwo Oyedele, ya yi nazari don gyaran fuska a harkokin kuɗi da garambawul a harkar tara haraji da kuma kyautata bunƙasar tattalin arziƙi a cikin shekara ɗaya.

Tinubu ya ce Najeriya har yanzu tana fuskantar ƙalubale a ɓangarorin da suka haɗar da biyan haraji cikin sauƙi, kuma kason haraji da take karɓa idan an kwatanta da kuɗin da take samu daga duk abin da ta sarrafa a gida ya yi kaɗan. A cewarsa ƙasar, ta zama kurar baya a Afirka a wannan ɓangare.

Sanarwar ta ce manufar shugaban ƙasar ita ce yi wa tsarin karɓar haraji gyaran fuska don tallafa wa bunƙasa harkokin ci gaba mai ɗorewa.

Ya ce matuƙar babu kuɗin shiga, gwamnati ba za ta iya samar isassun ayyukan inganta rayuwa ga al’ummar da suka ba ta amana ba.

Shugaba Tinubu ya ba da umarnin cewa ana sa ran kwamitin zai gabatar da wani tsarin garambawul cikin gaggawa da za a iya aiwatarwa a cikin kwana 30. Sai kuma ba da shawarwari kan muhimman sauye-sauye a cikin wata shida, aiwatar da cikakkun tsare-tsaren a cikin shekara ɗaya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp