Home Labarai Kotu ta kwace zaman Dan majalisa a jihar Kano

Kotu ta kwace zaman Dan majalisa a jihar Kano

Kotun sauraron ƙorafin zaɓe da ke zama a Kano ta soke zaɓen Honourable Muktar Umar Yarima mai wakiltar Tarauni a majalisar wakilai saboda amfani da takardu shaidar kammala karatu na bogi.

A hukuncin da alƙalan kotun uku suka bayar, sun ce sun samu Yarima da gabatar da takardar kammala karatun firamare na bogi, don haka kotun ta umarci hukumar zabe ta ƙasa ta ayyana ɗan takarar jam’iyyar APC, Honourable Hafizu Ibrahim Kawu a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

A baya dai jami’in sanar da sakamakon zaben mazabar Tarauni, a zaɓen da ya gabata, Garba Galadanci ya sanar da Yarima na jam’iyyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben, bayan samun ƙuri’a 26,273, ya kuma doke Honourable Hafizu Ibrahim Kawu na jam’iyyar APC wanda ya samu ƙuri’a 15,931.

Daga baya Kawu ya shigar da ƙara, inda ya ƙalubalanci sakamakon zaɓen a bisa zargin gabatar da takardun bogi daga ɓangaren wanda ya yi nasarar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp