Home DUNIYA ECOWAS na shirin Lashe amai kan Jamhuriyar Nijar

ECOWAS na shirin Lashe amai kan Jamhuriyar Nijar

Alamu na nuna cewa kungiyar ECOWAS na shirin janye barazanar amfani da karfin soji domin mayar da zababiyar gwamnatin a Jamhuriyar Nijar.

Wannan na zuwa ne bayan wata ganawa da kungiyar da mambobinta a birnin tarayyar Nijeriya aa batun juyin mulkin kasar.

A yayin taron kungiyar Kasashen Afrika ta Yamma, ta ce za ta ci gaba tintibar sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar a yunkurin da take na warware matsalar.

Yayin bude taro na musammman da shugabannin kungiyar a Abuja, shugaban ECOWAS Bola Ahmed Tinubu da ke jagorancin taron ya bayyana taron na yau a matsayin mai matukar muhimmanci wajen ci gaba da dorewar yankin a matsayin dunkulalle wanda zai ta taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da kuma ci gaban Al’umma.

Shugaban ya ce taronsu na yau zai bada damar cikakken nazari kan ci gaban da aka samu da kuma matsalolin da aka fuskanta tun bayan taron farko da suka yi kan Nijar, domin duba gyaran da ya kamata a yi ko kuma gibin da ya kamata a cike domin gyara lamarin.

Shugaban na ECOWAS ya ce ya zama wajibi a gare su a matsayin shugabanni su fahimci cewar halin da ake ciki a Nijar na zama barazana a gare su, kuma abin da ke iya biyo baya zai shafi yankin baki daya.

Tinubu ya bayyana fatar cewar wannan taro na biyu kan Nijar zai bada damar daukar matakin da ya dace wanda zai taimaka wa yankin baki daya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp