Home Labarai Wani sabon hari a jihar Filato yayi sanadiyar mutane 21

Wani sabon hari a jihar Filato yayi sanadiyar mutane 21

Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen  jihar Filato ta ce a ƙalla mutum 21 aka kashe a wani sabon hari da aka kai a ƙauyuka biyu a jihar.

Ƴan bindiga sun mamaye ƙauyen Barikin Ladi da sanyin safiyar Alhamis, inda suka harbe mutum 17.

Bayan wani ɗan lokaci an sake harbe mutum huɗu a wani harin da ƴan bindigar suka kai wani ƙauye da ke kusa da barikin ladin.

Kashe-kashen na zuwa ne a daidai lokacin da sojoji ke luguden wuta cikin dazukan da ke zargin maɓoya ce ta ƴan ta’adda a ƙoƙarin da gwamnati ke yi na kawo ƙarshen hare-haren da yayi sanadiyar mutuwar ɗaruruwan mutane tun daga watan Mayu.

Ƙungiyoyin fararen hula sun ɗora alhakin kashe-kashe kan makiyaya, inda suka ce suna yin hakan ne domin tarwatsa manoman yankin don samun damar mamaye filayensu.

Sai dai babu tabbaci ko ƙungiyoyin  makiyayan sun tofa albarkacin bakinsu kan wannan zargi.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp