Home DUNIYA ECOWAS ta bukaci AU da ta amince da kudirorin da ta dauka...

ECOWAS ta bukaci AU da ta amince da kudirorin da ta dauka kan Nijar

Kungiyar Kasashen Yammacin Afrika ta ECOWAS ta umarci rundunarta da ke cikin shirin-ko-ta-kwana da ta maido da kundin tsarin mulki a Jamhuriyar Nijar.

Shugaban gudanarwar ECOWAS Omar Alie Touray ya bayyana haka a lokacin da yake karanta kudirorin da kungiyar ta dauka game da juyin mulkin Nijar a wani taro da ya gudana birnin Abuja na Najeriya a wannan Alhamis.

ECOWAS ta bayyana cewa, ta dauki matsayar ce bayan ta nazarci rahoto da kuma shawarwarin da Kwamitin Hafsosshin Tsaronta ya bayar, tana mai korafin cewa, daukacin hanyoyin diflomasiyar da ta bi don warware rikicin siyasar kasar sun ci-tura sakamakon yadda sojojin suka yi juyin mulki suka ki mutunta umarnin da aka ba su.

ECOWAS ta bai wa sojojin na Nijar wa’adin ranar 6 ga wannan wata na Agusta da su mayar da shugaba Mohamed Bazoum kan kujerarsa ta shugaban kasa, amma suka ki mutunta wannan umarni.

Yanzu haka ECOWAS ta jaddada matsayarta ta yin Allah-wadai da juyin mulkin gami da ci gaba da tsare shugaba Bazoum da iyalansa da wasu jami’an gwamnatinsa.

Kungiyar ta kasashen yammacin Afrika ta sanar da tsaurara matakan rufe kan iyakokin Nijar da haramta tafiye-tafiye da daskarar da kadarorin wadanda ke da hannu a juyin mulkin bayan ta gaza magance rikicin kasar ta hanyar laluma.

A bangare guda, ECOWAS ta bukaci Kungiyar AU da ta amince da daukacin kudirorin da ta dauka a dalilin halin da ake ciki a Jamhuriyar Nijar.

Har ila yau, ECOWAS ta yi kira ga kasashen duniya aminanta da Majalisar Dinkin Duniya da su mara mata baya domin samun natija ta gaggawa dangane da maido da kundin tsarin mulki a Nijar.

Kawo yanzu dai, sojojin da suka yi juyin mulkin na Nijar ba su nuna wata alamar shiga tattaunawar fahimtar juna da ECOWAS ba duk kuwa da tarin takunkuman da aka malkaya musu baya ga barazanar daukar matakin sojin da aka yi musu.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp