Home DUNIYA ECOWAS ta bukaci AU da ta amince da kudirorin da ta dauka...

ECOWAS ta bukaci AU da ta amince da kudirorin da ta dauka kan Nijar

Kungiyar Kasashen Yammacin Afrika ta ECOWAS ta umarci rundunarta da ke cikin shirin-ko-ta-kwana da ta maido da kundin tsarin mulki a Jamhuriyar Nijar.

Shugaban gudanarwar ECOWAS Omar Alie Touray ya bayyana haka a lokacin da yake karanta kudirorin da kungiyar ta dauka game da juyin mulkin Nijar a wani taro da ya gudana birnin Abuja na Najeriya a wannan Alhamis.

ECOWAS ta bayyana cewa, ta dauki matsayar ce bayan ta nazarci rahoto da kuma shawarwarin da Kwamitin Hafsosshin Tsaronta ya bayar, tana mai korafin cewa, daukacin hanyoyin diflomasiyar da ta bi don warware rikicin siyasar kasar sun ci-tura sakamakon yadda sojojin suka yi juyin mulki suka ki mutunta umarnin da aka ba su.

ECOWAS ta bai wa sojojin na Nijar wa’adin ranar 6 ga wannan wata na Agusta da su mayar da shugaba Mohamed Bazoum kan kujerarsa ta shugaban kasa, amma suka ki mutunta wannan umarni.

Yanzu haka ECOWAS ta jaddada matsayarta ta yin Allah-wadai da juyin mulkin gami da ci gaba da tsare shugaba Bazoum da iyalansa da wasu jami’an gwamnatinsa.

Kungiyar ta kasashen yammacin Afrika ta sanar da tsaurara matakan rufe kan iyakokin Nijar da haramta tafiye-tafiye da daskarar da kadarorin wadanda ke da hannu a juyin mulkin bayan ta gaza magance rikicin kasar ta hanyar laluma.

A bangare guda, ECOWAS ta bukaci Kungiyar AU da ta amince da daukacin kudirorin da ta dauka a dalilin halin da ake ciki a Jamhuriyar Nijar.

Har ila yau, ECOWAS ta yi kira ga kasashen duniya aminanta da Majalisar Dinkin Duniya da su mara mata baya domin samun natija ta gaggawa dangane da maido da kundin tsarin mulki a Nijar.

Kawo yanzu dai, sojojin da suka yi juyin mulkin na Nijar ba su nuna wata alamar shiga tattaunawar fahimtar juna da ECOWAS ba duk kuwa da tarin takunkuman da aka malkaya musu baya ga barazanar daukar matakin sojin da aka yi musu.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp