Home Labarai Zamu kare Damukradiyya a Nijeriya – Sojojin Nijeriya

Zamu kare Damukradiyya a Nijeriya – Sojojin Nijeriya

Babban hafsan sojin Najeriya Laftanar Janar Taoreed Lagbaja ya ce babban abin da ya fi dacewa da ƙasar a wannan zamani shi ne mulkin dimokradiyya.

Babban hafsan sojin ya bayyana haka ne a lokacin bikin yaye manyan sojoji da aka gudanar da makarantar yaye manyan hafsoshi ta Jaji da ke Kaduna, kamar yadda wata sanarwa da kakakin rundunar Burgediya Janar Onyema Nwachukwu ya fitar.

Laftanar Janar Lagbaja ya ce dole ne a tunasar da sojojin ƙasar cewa taimakonsu wajen tabbatuwa da ɗorewar mulki shi ne babbar hanyar nuna ƙwarewa a aikin soji.

Ya kuma ce babban burin kowanne ɗan Najeriya a yanzu shi ne ɗorewar mulkin dimokradiyya, wanda zai tabbatar da haɗin kan ƙasa da kuma kare muradun ‘yan Najeriya, ba tare da la’akari da bambanci addini ko na ƙabila ba.

”A don haka ina kira ga duka sojojin Najeriya su bayar da gudunmowarsu wajen tabbatar da ɗorewar mulkin dimokraɗiyya, sannan su kauce wa shiga lamuran siyasa a lokacin gudanar da ayyukansu”, in babban hafsan sojojin.

Ya kuma jaddada burin rundunar sojin ƙasar na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ƙasar.

Laftanar Janar Lagbaja ya ce sojojin ƙasar tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaron ƙasar na aiki ba dare ba rana domin tabbatar da kare martabar ƙasar.

Babban hafsan sojin na wannan jawabi ne a daidai lokacin da ƙasashen ƙungiyar Ecowas suka bai wa sojojin da suka hamɓarar da gwamnatin farar hula ta Mohamed Bazoum a Nijar wa’adin mako guda na su mayar da shi kan mulki su fuskanci tarin takunkumai, ciki har da na matakin Soji.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp