Wani sabon hari a jihar Filato yayi sanadiyar mutane 21

Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen  jihar Filato ta ce a ƙalla mutum 21 aka kashe a wani sabon hari da aka kai a ƙauyuka biyu a jihar.

Ƴan bindiga sun mamaye ƙauyen Barikin Ladi da sanyin safiyar Alhamis, inda suka harbe mutum 17.

Bayan wani ɗan lokaci an sake harbe mutum huɗu a wani harin da ƴan bindigar suka kai wani ƙauye da ke kusa da barikin ladin.

Kashe-kashen na zuwa ne a daidai lokacin da sojoji ke luguden wuta cikin dazukan da ke zargin maɓoya ce ta ƴan ta’adda a ƙoƙarin da gwamnati ke yi na kawo ƙarshen hare-haren da yayi sanadiyar mutuwar ɗaruruwan mutane tun daga watan Mayu.

Ƙungiyoyin fararen hula sun ɗora alhakin kashe-kashe kan makiyaya, inda suka ce suna yin hakan ne domin tarwatsa manoman yankin don samun damar mamaye filayensu.

Sai dai babu tabbaci ko ƙungiyoyin  makiyayan sun tofa albarkacin bakinsu kan wannan zargi.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 32 minutes 26 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 13 minutes 51 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com