Home Labarai Wani sabon hari a jihar Filato yayi sanadiyar mutane 21

Wani sabon hari a jihar Filato yayi sanadiyar mutane 21

Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen  jihar Filato ta ce a ƙalla mutum 21 aka kashe a wani sabon hari da aka kai a ƙauyuka biyu a jihar.

Ƴan bindiga sun mamaye ƙauyen Barikin Ladi da sanyin safiyar Alhamis, inda suka harbe mutum 17.

Bayan wani ɗan lokaci an sake harbe mutum huɗu a wani harin da ƴan bindigar suka kai wani ƙauye da ke kusa da barikin ladin.

Kashe-kashen na zuwa ne a daidai lokacin da sojoji ke luguden wuta cikin dazukan da ke zargin maɓoya ce ta ƴan ta’adda a ƙoƙarin da gwamnati ke yi na kawo ƙarshen hare-haren da yayi sanadiyar mutuwar ɗaruruwan mutane tun daga watan Mayu.

Ƙungiyoyin fararen hula sun ɗora alhakin kashe-kashe kan makiyaya, inda suka ce suna yin hakan ne domin tarwatsa manoman yankin don samun damar mamaye filayensu.

Sai dai babu tabbaci ko ƙungiyoyin  makiyayan sun tofa albarkacin bakinsu kan wannan zargi.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp