Home Labarai Fadar shugaban Nijeriya ta musanta batun dawo da tallafin man fetur na...

Fadar shugaban Nijeriya ta musanta batun dawo da tallafin man fetur na wucin gadi.

Babban Mai Temakawa Shugaban Ƙasa a Kan Harkokin Yaɗa Labari da Hulɗa da Jama’a. Tope Ajayi, ya ce, babu wani shirin da gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu take yi na dawo da tallafin man fetur.

Ajayi ya yi wannan bayani ne a yau Alhamis a shafinsa na X wanda a baya ake kira da Twitter da misalin ƙarfe 6:08 agogon Najeriya.

Ya rubuta cewar, babu wani shiri na dawo da duk wani Nau’I na tallafi, sannan kuma babu wani yanayi da zai sa a goyi bayan duk wani tashin farashin a wannan lokacin.
Ya ƙara da cewar, Shugaban Ƙasa Tinubu ya gamsu da cewar, bisa bayanan da yake samu, za a iya ci gaba da kasancewa kan farashin da ake kai a yanzu haka.

Wannan rubutu na Ajayi dai ya zo ne, biyo bayan labaran da suke cewa, an ɗan dawo da tallafin man fetur saboda ƙaruwar kuɗin shigo da shi wanda ya samo asali daga faɗuwar darajar naira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp