Fadar shugaban Nijeriya ta musanta batun dawo da tallafin man fetur na wucin gadi.

Babban Mai Temakawa Shugaban Ƙasa a Kan Harkokin Yaɗa Labari da Hulɗa da Jama’a. Tope Ajayi, ya ce, babu wani shirin da gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu take yi na dawo da tallafin man fetur.

Ajayi ya yi wannan bayani ne a yau Alhamis a shafinsa na X wanda a baya ake kira da Twitter da misalin ƙarfe 6:08 agogon Najeriya.

Ya rubuta cewar, babu wani shiri na dawo da duk wani Nau’I na tallafi, sannan kuma babu wani yanayi da zai sa a goyi bayan duk wani tashin farashin a wannan lokacin.
Ya ƙara da cewar, Shugaban Ƙasa Tinubu ya gamsu da cewar, bisa bayanan da yake samu, za a iya ci gaba da kasancewa kan farashin da ake kai a yanzu haka.

Wannan rubutu na Ajayi dai ya zo ne, biyo bayan labaran da suke cewa, an ɗan dawo da tallafin man fetur saboda ƙaruwar kuɗin shigo da shi wanda ya samo asali daga faɗuwar darajar naira.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 31 minutes 18 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 12 minutes 43 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com