Tinubu ya nada shuwagabannin NTA, VON, FRCN

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya nada Sabbin shuwagabanni hukumomi da ma’aikatun 8 dake karkashin hukumar sadarwa da wayar da kai ta kasar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mashawarci kan yada labarai ga shugaban kasar Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu a birnin tarayya Abuja.

Sanarwar tace an nada: According to the statement those appointed are:

(1). Mr. Lanre Issa-Onilu matsayin shugaban hukumar wayar da kai ta (NOA)

(2) Mr. Salihu Abdulhamid Dembos matsayin shugaban gidan Talabijin na kasa  (NTA).

(3) Dr. Muhammed Bulama matsayin shugaban gidajen Radio Gwamantin Tarayya  (FRCN).

(4) Mr. Charles Ebuebu matsayin shugaban hukumar dake lura da kafafen yada labarai na Nijeriya (NBC).

(5) Mr. Jibrin Baba Ndace matsayin shugaban kafar yada labarai ta  (VON)

(6) Dr. Lekan Fadolapo shugaban hukumar dake lura da tallace-tallace a kafafen yada labarai ta (ARCON).

(7) Mr. Ali Muhammed Ali matsayin shugaban kamfanin dillancin Labarai na Nijeriya News (NAN).

(8) Mr. Dili Ezughah matsayin shugaban (NPC).

Sanarwa ta bayyana cewa Tinubu ya bukaci sabbin shuwagabannin dasu zama masu amfani da fikira wajen ciyar da inda aka dora musu nauyin lura dashi gaba, tare da jagorori na kwarai.

Ta kuma cewa nadin nasu ya fara aiki nan take.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 38 minutes 37 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 20 minutes 2 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com