Home Labarai Obasanjo ya kalubalnaci hukuncin kotu kan zaben Gwamnoni

Obasanjo ya kalubalnaci hukuncin kotu kan zaben Gwamnoni

Tsohon shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo ya caccaki hukuncin da alƙalan Najeriya suka yanke kan shari’o’in zaɓe, yana mai cewa bai kamata alƙalai uku zuwa biyar su soke hukuncin da miliyoyin masu kada ƙuri’a suka yanke a lokacin zabe ba.

Obasanjo ya bayyana ikon da wasu alƙalai ƙalilan ke da shi a matsayin al’amari da “ba za a amince da shi ba.”

Tsohon shugaban ƙasar ya yi magana ne dangane da hukuncin da kotun ɗaukaka ƙara ke ci gaba da yi kan taƙaddamar zaɓe ta bayan zaɓen 2023 a Najeriya.

A makon da ya gabata ne dai wasu alƙalan kotun ɗaukaka ƙara suka yanke hukuncin korar wasu gwamnoni uku daga aiki.

Lokacin da yake tsokaci a wani taro sake fasalin dimokuraɗiyya domin amfanin ƙasashen Afirka, a garin Abeokuta na jihar Ogun, ya ce tsarin mulkin dimokuraɗiyya na ƙasashen yamma ba zai taɓa yin daidai da ƙasashen Afirka ba kasancewar ba ya la’akari da ra’ayin mafi yawan al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp