Home Labarai ‘Yan sandan Sun hallaka ‘yan bindiga 50 a Jihar Taraba

‘Yan sandan Sun hallaka ‘yan bindiga 50 a Jihar Taraba

rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa an hallaka ‘yan bindiga fiye da 50 da ake zargin su ne ke addabar karamar hukumar Bali ta Jihar Taraba.

Rundunar ƴan sanda a jihar ce ta bayyana haka ta bakin Kakakin ta Abdullahi Usman ta shaida hakan a ranar Alhamis cewa jami’an ‘yan sanda tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro ne suka kashe ‘yan fashin dajin.

Ya ce aikin hadin gwiwar ya zo ne bayan korafe-korafe da mutanen yankin suka yi wanda ya kai ga yi wa ƴan fashin kwanton bauna tare da halaka  su.

“Rundunar ‘yan sandan jihar Taraba ta samu labarin cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba, amma dai ana zargin masu garkuwa da mutane ne, daruruwan su sun kai farmaki kauyen Tonti da ke karkashin gundumar Maihula cikin karamar hukumar Bali a jihar Taraba.

“‘Yan bindigan sun kai farmaki kauyen ne da misalin karfe 5:30, kuma suka fara harbe-harbe,” kamar yadda ya shaida wa Channels.

“Da samun bayanai, kwamishinan ‘yan sandan Taraba, Joseph Eribo, ya bayar da umarnin tura wata zugar jami’an tsaro daga reshen Bali zuwa yankin ciki har da hadin gwiwar sojoji da ‘yan banga, da mafarauta.”

Ya ce suna ci gaba da farautar ‘yan ta’addan da suka tsere, kuma an tura wata runduna ta musamman domin inganta tsaro a yankin.

Sai dai ya kara da cewa: “Wani abin takaici shi ne ‘yan bindigan sun harbe mutanen yankin 12 kafin jami’an tsaro su isa”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp