Home Labarai Jirgin sojin saman Nijeriya ya yi hadari

Jirgin sojin saman Nijeriya ya yi hadari

Nigeria Airforce

Wani helikwaftan rundunar sojojin saman Najeriya ya yi hatsari a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas da safiyar yau Juma’a.

Mai magana da yawun rundunar, Edward Gabkwet ne, ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce dukkan wadanda ke cikin jirgin sun kubuta, ko da yake sun samu “kananan raunuka”.

Jirgin helikwaftan kirar MI-35P ya yi hatsari ne da misalin karfe 7.45 na safe, jim kadan bayan ya tashi a kan hanyarsa ta zuwa yaki da masu zangon ƙasa ga tattalin arzikin kasa da ke fasasa bututu suna satar man fetur a jihar Ribas.

“Abin farin cikin shi ne dukkan ma’aikatan jirgin 5 sun kubuta da rayukansu, sai dai kananan raunuka kuma a halin yanzu ana kula da su a wani asibitin sojoji da ke Fatakwal.

“Babban hafsan sojojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar, a halin yanzu yana kan hanyarsa ta zuwa Fatakwal, don ganin halin da ake ciki da kansa, kuma da niyyar duba lafiyar ma’aikata,” in ji sanarwar.

ana ganin yawaitar hatsari da jiragen saman sojin Najeriya ke yi wanda ke janyo asarar rayuka, ya zama abin damuwa matuƙa a cikin shekara biyu, inda masu ruwa da tsaki suka yi kira ga sojoji, su kiyaye hanyoyin gudanar da ayyukansu da kuma kula da jiragensu na yau da kullum.

A watan Agustan 2023 ma, jirgin saman sojin Najeriya NAF MI-171 ya yi hatsari a kusa da kauyen Chukuba na jihar Neja, inda ya haddasa asarar sojoji.

A 2021, sojoji akalla 20 ne suka rasu cikin wata uku a hadurra uku na jiragen saman sojin Najeriya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp