Home Labarai Jirgin sojin saman Nijeriya ya yi hadari

Jirgin sojin saman Nijeriya ya yi hadari

Nigeria Airforce

Wani helikwaftan rundunar sojojin saman Najeriya ya yi hatsari a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas da safiyar yau Juma’a.

Mai magana da yawun rundunar, Edward Gabkwet ne, ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce dukkan wadanda ke cikin jirgin sun kubuta, ko da yake sun samu “kananan raunuka”.

Jirgin helikwaftan kirar MI-35P ya yi hatsari ne da misalin karfe 7.45 na safe, jim kadan bayan ya tashi a kan hanyarsa ta zuwa yaki da masu zangon ƙasa ga tattalin arzikin kasa da ke fasasa bututu suna satar man fetur a jihar Ribas.

“Abin farin cikin shi ne dukkan ma’aikatan jirgin 5 sun kubuta da rayukansu, sai dai kananan raunuka kuma a halin yanzu ana kula da su a wani asibitin sojoji da ke Fatakwal.

“Babban hafsan sojojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar, a halin yanzu yana kan hanyarsa ta zuwa Fatakwal, don ganin halin da ake ciki da kansa, kuma da niyyar duba lafiyar ma’aikata,” in ji sanarwar.

ana ganin yawaitar hatsari da jiragen saman sojin Najeriya ke yi wanda ke janyo asarar rayuka, ya zama abin damuwa matuƙa a cikin shekara biyu, inda masu ruwa da tsaki suka yi kira ga sojoji, su kiyaye hanyoyin gudanar da ayyukansu da kuma kula da jiragensu na yau da kullum.

A watan Agustan 2023 ma, jirgin saman sojin Najeriya NAF MI-171 ya yi hatsari a kusa da kauyen Chukuba na jihar Neja, inda ya haddasa asarar sojoji.

A 2021, sojoji akalla 20 ne suka rasu cikin wata uku a hadurra uku na jiragen saman sojin Najeriya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp