Home Labarai ‘Yan sandan Sun hallaka ‘yan bindiga 50 a Jihar Taraba

‘Yan sandan Sun hallaka ‘yan bindiga 50 a Jihar Taraba

rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa an hallaka ‘yan bindiga fiye da 50 da ake zargin su ne ke addabar karamar hukumar Bali ta Jihar Taraba.

Rundunar ƴan sanda a jihar ce ta bayyana haka ta bakin Kakakin ta Abdullahi Usman ta shaida hakan a ranar Alhamis cewa jami’an ‘yan sanda tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro ne suka kashe ‘yan fashin dajin.

Ya ce aikin hadin gwiwar ya zo ne bayan korafe-korafe da mutanen yankin suka yi wanda ya kai ga yi wa ƴan fashin kwanton bauna tare da halaka  su.

“Rundunar ‘yan sandan jihar Taraba ta samu labarin cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba, amma dai ana zargin masu garkuwa da mutane ne, daruruwan su sun kai farmaki kauyen Tonti da ke karkashin gundumar Maihula cikin karamar hukumar Bali a jihar Taraba.

“‘Yan bindigan sun kai farmaki kauyen ne da misalin karfe 5:30, kuma suka fara harbe-harbe,” kamar yadda ya shaida wa Channels.

“Da samun bayanai, kwamishinan ‘yan sandan Taraba, Joseph Eribo, ya bayar da umarnin tura wata zugar jami’an tsaro daga reshen Bali zuwa yankin ciki har da hadin gwiwar sojoji da ‘yan banga, da mafarauta.”

Ya ce suna ci gaba da farautar ‘yan ta’addan da suka tsere, kuma an tura wata runduna ta musamman domin inganta tsaro a yankin.

Sai dai ya kara da cewa: “Wani abin takaici shi ne ‘yan bindigan sun harbe mutanen yankin 12 kafin jami’an tsaro su isa”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp