sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga a jihar Sokoto

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta hallaka wasu ‘yan bindiga tare da kuɓutar da wasu mutane da suke garkuwa da su a jihar Sokoto.

Cikin wani saƙo da rundunar sojin ƙasar ta wallafa a shafinta na X, ta ce cikin wani hari da dakarunta na Hadarin Daji suka kaddamar a kauyen Bauni da dajin Bauni a jihar ranar 14 ga watan Disamba, inda sojojin suka shafe sa’o’i masu yawa suna musayar wuta da ‘yan bindigar.

Sanarwar ta ce bayan da sojojin suka matsa wa ‘yan bindigar, sai suka tsere tare da barin maɓoyarsu, lamarin da ya sa sojojin suka samu nasarar kuɓutar da mutum shida da suke garkuwa da su.

”Sai dai kafin tserewar ‘yan bindigar, sojojin sun kashe uku daga cikinsu, tare da gano makamai”, in ji sanarwar.

Makaman da aka gano sun haɗar da bindiga ƙirar AK-47 biyu da kuttun adana alburusai 19, da alburusai, da bindigogin toka biyu d babura, da na’urorin oba-oba da sauran kayayyaki

Sanarwar ta ce sojojin sun lalata maɓoyar ‘yan bindigar tare da babuwarn da suka gano nan take.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 8 minutes 57 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 50 minutes 22 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com