Home Labarai A ɗauki matakan tabbatar da amincin mata da ‘yan mata a Najeriya...

A ɗauki matakan tabbatar da amincin mata da ‘yan mata a Najeriya – UNICEF

Najeriya ta bi sahun ƙasashen duniya wajen gudanar da bikin gangamin yaƙi da zin zarafi mai nasaba da jinsi,da ƙungiyar Unicef ke jagoranta.

Gangamin na bana- mai taken ”zuba kuɗaɗe don yaƙi da cin zarafin mata da ‘yan mata” – ya jaddada ƙudurin gwamnati na magance duka nau’ikan cin zarafin mata da ƙananan yara.

Taron na bana – wanda aka kwashe kwanaki 16 ana gudanarwa ya ƙarfafa wa mutane gwiwa wajen bayyana ƙudurinsu don magance matsalar cin zarafin mata da ‘yan mata ta hanyar musayar matakan da ake ɗauka don magance matsalar a faɗin duniya.

Haka kuma gangamin ya kuma buƙaci gwamnatoci da hukumomin duniya da su bayyana irin jarin da suke zuba wa don magance matsalar cin zarafin jinsi.

Cikin wata sanarwar ta Unifef ta fitar bayan taron, ta ce nau’ikan cin zarafin jinsi da ake aikatawa a Najeriya sun haɗar da fyaɗe da cin zarafin matan aure, da aikata lalata da auren wuri da kaciyar ‘ya’ya mata da sauran abubuwa, lamarin da ke tasiri ga matan ta fuskar tunani da zamantakewa da tattalin arzikinsu.

Sanarwar ta ce gwamnatin Najeriya ƙarƙashin ma’aikatar lafiya da ma’aikatar harkokin mata, sun haɗa hannu da hukumar Unicef da sauran masu ruwa da tsaki wajen wayar da kan al’umma wajen magance matsalolin da suka jiɓanci cin zarafin mata.

Wakiliyar Unicef a Najeriya, Cristian Munduate ta ce ”a hukumarmu mun fahimci cewa magance matsalar cin zarafin mata da ‘yan mata ba abu ne da ke buƙatar gaggawa ba, babbar buƙatarmu ita ce aiki da gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki don magance matsalar tun daga tushe. A yanzu lokacin ɗaukar mataki ya yi, domin tabbatar da cewa mata da ‘yan mata sun rayu cikin aminci da karimci da girmamawa tare da ‘yanci”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp