Home Labarai CBN ya dakatar da karɓar kuɗi ga masu ajiya sama da 500,000

CBN ya dakatar da karɓar kuɗi ga masu ajiya sama da 500,000

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya dakatar da karbar kuɗi daga masu ajiye kuɗi a asusunsu na banki, waɗanda suka kai sama da naira 500,000, daga yanzu har zuwa ranar 30 ga Afrilu, 2024.

Babban Bankin ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin mai dauke da sa hannun mukaddashin daraktan sanya ido kan harkokin bankuna, Adetona Adedeji.

A shekara ta 2019, babban bankin ya bayyana cewa zai fara cire wa masu mu’ammala da banki kuɗi a lokacin da za su cire ko ajiye kuɗi a banki a wani bangare na kokarinsa na rage amfani da tsabar kuɗi.

A baya, babban bankin ya umarci bankuna su riƙa karbar kashi biyar bisa dari na kudaden da za a cire da kuma kashi uku cikin dari na kuɗaɗen da za a ajiye sama da naira miliyan uku.

Sai dai, a cikin sabon umarnin da ya bayar, babban bankin ya ce, ya kamata bankunan su karbi dukkan kudaden da jama’a ke ajiyewa a banki ba tare da wani caji ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp