Home Labarai CBN ya dakatar da karɓar kuɗi ga masu ajiya sama da 500,000

CBN ya dakatar da karɓar kuɗi ga masu ajiya sama da 500,000

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya dakatar da karbar kuɗi daga masu ajiye kuɗi a asusunsu na banki, waɗanda suka kai sama da naira 500,000, daga yanzu har zuwa ranar 30 ga Afrilu, 2024.

Babban Bankin ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin mai dauke da sa hannun mukaddashin daraktan sanya ido kan harkokin bankuna, Adetona Adedeji.

A shekara ta 2019, babban bankin ya bayyana cewa zai fara cire wa masu mu’ammala da banki kuɗi a lokacin da za su cire ko ajiye kuɗi a banki a wani bangare na kokarinsa na rage amfani da tsabar kuɗi.

A baya, babban bankin ya umarci bankuna su riƙa karbar kashi biyar bisa dari na kudaden da za a cire da kuma kashi uku cikin dari na kuɗaɗen da za a ajiye sama da naira miliyan uku.

Sai dai, a cikin sabon umarnin da ya bayar, babban bankin ya ce, ya kamata bankunan su karbi dukkan kudaden da jama’a ke ajiyewa a banki ba tare da wani caji ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp