Home Labarai CBN ya dakatar da karɓar kuɗi ga masu ajiya sama da 500,000

CBN ya dakatar da karɓar kuɗi ga masu ajiya sama da 500,000

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya dakatar da karbar kuɗi daga masu ajiye kuɗi a asusunsu na banki, waɗanda suka kai sama da naira 500,000, daga yanzu har zuwa ranar 30 ga Afrilu, 2024.

Babban Bankin ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin mai dauke da sa hannun mukaddashin daraktan sanya ido kan harkokin bankuna, Adetona Adedeji.

A shekara ta 2019, babban bankin ya bayyana cewa zai fara cire wa masu mu’ammala da banki kuɗi a lokacin da za su cire ko ajiye kuɗi a banki a wani bangare na kokarinsa na rage amfani da tsabar kuɗi.

A baya, babban bankin ya umarci bankuna su riƙa karbar kashi biyar bisa dari na kudaden da za a cire da kuma kashi uku cikin dari na kuɗaɗen da za a ajiye sama da naira miliyan uku.

Sai dai, a cikin sabon umarnin da ya bayar, babban bankin ya ce, ya kamata bankunan su karbi dukkan kudaden da jama’a ke ajiyewa a banki ba tare da wani caji ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp