Home Labarai Sojojin Nijeriya Sun kubutar da Muutane 9 a jihar Kaduna.

Sojojin Nijeriya Sun kubutar da Muutane 9 a jihar Kaduna.

Dakarun sojojin Nijeriya na shiyya ta 1 sun sami nasarar kubutar da mutane 9 wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su tare da kwato makamai a karamar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna.

mukaddashin mai magana da yawun rundunar Lt. Col Musa Yahaya ne ya bayyana hakan inda yace mutanen sun shaki iskar ‘yancin ne a ranar 8 ga watan Disamba.

Yahaya ta cikin sanarwar da ya fitar ranar litinin a jihar Kaduna ya ce dakarun da aka girke a Birnin Yero na gudanar da atisaye a kanzaure, in suka sami labarin cewa ‘yan bindiagra sun yi garkuwa da mutane 11 a kauyukan Anguwar Maharba da Dandami.

ya kara da cewa dakarun dake aikin hadin gwiwa da rundunar tsaro ta JTF, sun sami nasarar kai harin kan ‘yan ta’adda a maboyar su.

“dakarun mu sun yi bata kashi da ‘yan bindigar, inda karfin wuta da matsa kaimi daga dakrun ya sanya dole ‘yna ta’addan suka gudu tare da raunikan harbin bindiga a jukkunan su.

“Sojojin sun sami nasarar kubutar da mutane 9 da ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da su, yayin da ‘yan bindigan suka hallaka mutane 2 kafin isar dakarun.”

ya ce sun sami nasara kwato bindiga kirar AK47 da alburusai, da bindiga kirar gida.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp