Home Labarai Sojojin Nijeriya Sun kubutar da Muutane 9 a jihar Kaduna.

Sojojin Nijeriya Sun kubutar da Muutane 9 a jihar Kaduna.

Dakarun sojojin Nijeriya na shiyya ta 1 sun sami nasarar kubutar da mutane 9 wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su tare da kwato makamai a karamar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna.

mukaddashin mai magana da yawun rundunar Lt. Col Musa Yahaya ne ya bayyana hakan inda yace mutanen sun shaki iskar ‘yancin ne a ranar 8 ga watan Disamba.

Yahaya ta cikin sanarwar da ya fitar ranar litinin a jihar Kaduna ya ce dakarun da aka girke a Birnin Yero na gudanar da atisaye a kanzaure, in suka sami labarin cewa ‘yan bindiagra sun yi garkuwa da mutane 11 a kauyukan Anguwar Maharba da Dandami.

ya kara da cewa dakarun dake aikin hadin gwiwa da rundunar tsaro ta JTF, sun sami nasarar kai harin kan ‘yan ta’adda a maboyar su.

“dakarun mu sun yi bata kashi da ‘yan bindigar, inda karfin wuta da matsa kaimi daga dakrun ya sanya dole ‘yna ta’addan suka gudu tare da raunikan harbin bindiga a jukkunan su.

“Sojojin sun sami nasarar kubutar da mutane 9 da ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da su, yayin da ‘yan bindigan suka hallaka mutane 2 kafin isar dakarun.”

ya ce sun sami nasara kwato bindiga kirar AK47 da alburusai, da bindiga kirar gida.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp