Home Labarai Sojojin Nijeriya Sun kubutar da Muutane 9 a jihar Kaduna.

Sojojin Nijeriya Sun kubutar da Muutane 9 a jihar Kaduna.

Dakarun sojojin Nijeriya na shiyya ta 1 sun sami nasarar kubutar da mutane 9 wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su tare da kwato makamai a karamar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna.

mukaddashin mai magana da yawun rundunar Lt. Col Musa Yahaya ne ya bayyana hakan inda yace mutanen sun shaki iskar ‘yancin ne a ranar 8 ga watan Disamba.

Yahaya ta cikin sanarwar da ya fitar ranar litinin a jihar Kaduna ya ce dakarun da aka girke a Birnin Yero na gudanar da atisaye a kanzaure, in suka sami labarin cewa ‘yan bindiagra sun yi garkuwa da mutane 11 a kauyukan Anguwar Maharba da Dandami.

ya kara da cewa dakarun dake aikin hadin gwiwa da rundunar tsaro ta JTF, sun sami nasarar kai harin kan ‘yan ta’adda a maboyar su.

“dakarun mu sun yi bata kashi da ‘yan bindigar, inda karfin wuta da matsa kaimi daga dakrun ya sanya dole ‘yna ta’addan suka gudu tare da raunikan harbin bindiga a jukkunan su.

“Sojojin sun sami nasarar kubutar da mutane 9 da ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da su, yayin da ‘yan bindigan suka hallaka mutane 2 kafin isar dakarun.”

ya ce sun sami nasara kwato bindiga kirar AK47 da alburusai, da bindiga kirar gida.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp