Dakarun sojojin Nijeriya na shiyya ta 1 sun sami nasarar kubutar da mutane 9 wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su tare da kwato makamai a karamar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna.
mukaddashin mai magana da yawun rundunar Lt. Col Musa Yahaya ne ya bayyana hakan inda yace mutanen sun shaki iskar ‘yancin ne a ranar 8 ga watan Disamba.
Yahaya ta cikin sanarwar da ya fitar ranar litinin a jihar Kaduna ya ce dakarun da aka girke a Birnin Yero na gudanar da atisaye a kanzaure, in suka sami labarin cewa ‘yan bindiagra sun yi garkuwa da mutane 11 a kauyukan Anguwar Maharba da Dandami.
Read Also:
ya kara da cewa dakarun dake aikin hadin gwiwa da rundunar tsaro ta JTF, sun sami nasarar kai harin kan ‘yan ta’adda a maboyar su.
“dakarun mu sun yi bata kashi da ‘yan bindigar, inda karfin wuta da matsa kaimi daga dakrun ya sanya dole ‘yna ta’addan suka gudu tare da raunikan harbin bindiga a jukkunan su.
“Sojojin sun sami nasarar kubutar da mutane 9 da ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da su, yayin da ‘yan bindigan suka hallaka mutane 2 kafin isar dakarun.”
ya ce sun sami nasara kwato bindiga kirar AK47 da alburusai, da bindiga kirar gida.
PRNigeria Hausa










