Kotun kolin Nijeriya ta sanya ranar sauraren karar Gwamnan Kano

Kotun Ƙolin Najeriya ta sanya ranar Alhamis, 21 ga watan Disamba domin sauraron ƙarar da aka shigar kan zaɓen gwamnan jihar Kano.

Gwamna Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP na kalubalantar hukuncin kotun daukaka ƙara da ta tabbatar da hukuncin kotun sauraran ƙararrakin zabe da ta soke nasararsa tare da bayyana Nasiru Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar na ranar 11 ga Maris.

Wannan ne karon farko da kotun za ta fara zama, inda za ta fara jin bahasi, yayin da har yanzu akwai muhimman takardun da ba a kai wa kotun ba.

Kotun ɗaukaka ƙara ta yanke hukuncin cewa Gwamna Yusuf ba dan jam’iyyar NNPP ba ne a lokacin da ya tsaya takarar gwamna.

Amma tabbataccen kwafin hukuncin, wanda ya bayyana kwanaki kaɗan bayan zaman kotun, ya kunshi bayanai masu karo da juna game da hukuncin da ya janyo ce-ce-ku-ce.

Duka bangarorin biyu dai sun yi ikirarin cewa hukuncin ya tabbatar da nasarar da suka samu a zaben.

Sai dai jam’iyyar NNPP ta shigar da ƙara a gaban kotun ƙoli, inda take ƙalubalantar hukuncin kotun daukaka ƙara da ta tabbatar da hukuncin kotun sauraron ƙararrakin zaben gwamna.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1187 days 17 hours 57 minutes 0 second,

Baptist School Students, Kaduna
1169 days 19 hours 38 minutes 25 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com