Home Labarai Emefiele ya cika ka’idar Beli

Emefiele ya cika ka’idar Beli

Tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya koma gida bayan ya cika sharuɗɗan belin da kotu ta ba shi.

Mai magana da yawun Gidan Yari na Kuje da ke Abuja, inda aka tsare Mista Emefiele, ya tabbatar da cewa an saki tsohon gwamnan a yammacin Juma’a.

Tun a ranar 22 ga watan Nuwamba ne Babbar Kotun Tarayya ta ba da belinsa kan naira miliyan 300 tare da gabatar da mutum biyu da ke da kadarori a unguwar Maitama da ke birnin na Abuja. Haka nan, kotun ta umarce shi da miƙa mata dukkan takardunsa na tafiye-tafiye.

Lamarin na zuwa ne bayan wani rahoto da mai bincke na musamman, Jim Obazee, ya zarge shi da karya dokar kwangila da sayen kayayyakin gwamnati.

Rahoton Obazee, wanda Shugaba Bola Tinubu ya naɗa a watan Yuli don ya binciki CBN a ƙarƙashin mulkin Emefiele, ya zarge shi da amfani da wakilansa wajen sayen Bankin Union, da kuma yin amfani da ƙarfin ikonsa a cinikin bankunan Polaris da Keystone.

Gwamnatin Tinubu na zargin tsohon gwamnan wanda ta dakatar a watan Yuni da aikata almundahanar kuɗi naira biliyan 1.2, zargin da ya musanta.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp