Tinubu ya mika Ta’aziyya ga Al’ummar jihar Filato

 Shugaban Nijeriya Bola Ahmad ya yi Allah-wadai da Harrin ‘yan bindiga a kananan hukumomin Bukkos da Barkin-Ladi dake Jihar Filato wanda yayi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

Wannan dai na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai taimakawa shugaban kasar ta a fannin yada labarai Chief Ajuri Ngelale.

Sanarwar tace shugaba Tinubu ya bayar da umarni ga jami’an tsaro, dasu gaggauta binciko wadanda ke da hannu a wannan lamari.

Haka Kuma Tinubu ya bayar da umarnin gaggauta bayar da tallafin gaggawa ga wadanda suka jikkata sakamakon aukuwar lamarin da kulawar magunguna.

Daga bisani shugaban kasar ya mika ta’aziyar sa ga Gwamnatin Jihar, tare tabbatar da Al’ummar jihar da Nijeriya baki daya cewa za a tabbatar da an an yiwa wadanda lamarin ya rutsa da su.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 34 minutes 49 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 16 minutes 14 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com