Home Labarai Kananan hukumomin Kano sun Maka Gwamnatin jihar a gaban kotu

Kananan hukumomin Kano sun Maka Gwamnatin jihar a gaban kotu

Shuwagabannin Kananan hukumomin Kano 44 sun Maka Gwamnatin jihar a gaban kotun tarayya Bisa Zargin ta da Kokarin dibar kudinsu Domin Tayi Aikin Wasu Gadoji a birnin jihar.

A ta cikin takardar Karar mai Lamba FHC/ABJ/CS/1733/2023, Shuwagabannin Kananan Hukumomin Sunyi Karar Gwamnatin Kano ne, Da Kwamishinan Shari’a Na jihar dama Akanta Janar na jihar.

Wannan na matsayin wani matakai kan yunkurin gwamnatin jihar na taba musu kudadensu na cikin asusun hadaka da sukeyi da ita (Joint Account) sakamakon abinda sukace ana kokarin dibar kudin a aikin gadojin Dan Agundi da ta Tal’udu.

Takardar mai Dauke da Kwanan Watan Jumu’a 29 Ga Watan Disambar ta Roki Kotun Data Hana Gwamnatin Kano Taba musu Kudin domin yin aikin gadojin Guda Biyu.

PRNigeria ta tabbatar da ganin ya  Shirye-Shiryen Gwamnatin Kano yayi nisa Wajen Fara ayyukan Guda Biyu.

PRNigeria hausa

 

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp