Home Labarai Abba Gida-gida ya kaddamar da ayyukan sabbin gadoji

Abba Gida-gida ya kaddamar da ayyukan sabbin gadoji

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya aza harsashin ginin gada mai hawa uku da zata lashe Naira biliyan 27  a mahadar Dan’agundi, da kuma Tal’udu duk a cikin birnin Kano.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labaran gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin tofa ya fitar kuma aka raba manema labarai a jihar.

A yayin a aza harsashin ginin, gwamnan ya ce an fara gudanar da manyan ayyukan ne domin rage cunkoson ababen hawa, da saukaka zirga-zirga, da kawata birnin, da hana gurbatar muhalli, da samar da ababen more rayuwa ga al’umma.

Haka Kuma gwamnan ya nanata alkawuran gwamnatinsa na samar da ababen more rayuwa a jihar tare da kudurin samar da karin ribar dimokuradiyya musamman ga wadanda aka zalunta.

Ya ce  matsayin jihar na babban birni ta cancanci a samar da gagarumin sauyi na ababen more rayuwa domin biyan bukatun mazauna birnin sama da miliyan goma da inganta zamantakewa da tattalin arzikin mazauna birnin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp