Home Labarai Ƴan sanda sun kuɓutar da malamin jami’ar jihar Nasarawa

Ƴan sanda sun kuɓutar da malamin jami’ar jihar Nasarawa

Rundunar ƴan sanda a jihar Nasarawa ta ce sun ceto wani malamin jami’ar jihar da ke Keffi, Isaac Igbawua daga hannun masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa.

wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin ƴan sandan jihar, Ramhan Nansel ya fitar aka kuma raba manema labarai

Ya ce jami’an rundunar ce tare da haɗin gwiwar ƴan bijilanti suka kuɓutar da malamin a wani kauye mai suna Ogba, a karamar hukumar Nasarawa Eggon da ke jihar.

An sace Igbawua, wanda malami ne a sashin kimiyyar ƙananan halittu (Microbiology) ranar 27 ga watan Disamba a karamar hukumar Kokona.

Kwana guda bayan sace shi, rundunar ƴan sandan jihar ta Nasarawa ta kama wani ɗalibin Jami’ar Tarayya da ke Lafiya, Daniel Favour Chukwuebuka, tare da kwato bindiga da harsashi a wajen da yake zama.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp