Home Labarai Ƴan sanda sun kuɓutar da malamin jami’ar jihar Nasarawa

Ƴan sanda sun kuɓutar da malamin jami’ar jihar Nasarawa

Rundunar ƴan sanda a jihar Nasarawa ta ce sun ceto wani malamin jami’ar jihar da ke Keffi, Isaac Igbawua daga hannun masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa.

wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin ƴan sandan jihar, Ramhan Nansel ya fitar aka kuma raba manema labarai

Ya ce jami’an rundunar ce tare da haɗin gwiwar ƴan bijilanti suka kuɓutar da malamin a wani kauye mai suna Ogba, a karamar hukumar Nasarawa Eggon da ke jihar.

An sace Igbawua, wanda malami ne a sashin kimiyyar ƙananan halittu (Microbiology) ranar 27 ga watan Disamba a karamar hukumar Kokona.

Kwana guda bayan sace shi, rundunar ƴan sandan jihar ta Nasarawa ta kama wani ɗalibin Jami’ar Tarayya da ke Lafiya, Daniel Favour Chukwuebuka, tare da kwato bindiga da harsashi a wajen da yake zama.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp