Rundunar ƴan sanda a jihar Nasarawa ta ce sun ceto wani malamin jami’ar jihar da ke Keffi, Isaac Igbawua daga hannun masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa.
wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin ƴan sandan jihar, Ramhan Nansel ya fitar aka kuma raba manema labarai
Read Also:
Ya ce jami’an rundunar ce tare da haɗin gwiwar ƴan bijilanti suka kuɓutar da malamin a wani kauye mai suna Ogba, a karamar hukumar Nasarawa Eggon da ke jihar.
An sace Igbawua, wanda malami ne a sashin kimiyyar ƙananan halittu (Microbiology) ranar 27 ga watan Disamba a karamar hukumar Kokona.
Kwana guda bayan sace shi, rundunar ƴan sandan jihar ta Nasarawa ta kama wani ɗalibin Jami’ar Tarayya da ke Lafiya, Daniel Favour Chukwuebuka, tare da kwato bindiga da harsashi a wajen da yake zama.
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1190 days 11 hours 47 minutes 57 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 29 minutes 22 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com