Home Labarai NDLEA ta kama sama da mutane dubu 1 a Kano

NDLEA ta kama sama da mutane dubu 1 a Kano

Hukumar dake hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa reshen jihar Kano NDLEA, tace ta samu nasarar cafke mutane 1,016 da ake zargin su da tu’ammali da miyagun kwayoyi a cikin shekarar 2023 da muka yi bankwana da ita.

Mai magana da yawun hukumar Sadiq Muhammad Maigatari shi ne ya bayyana hakan, inda yace mutanen da aka kama sun hadar da mata guda 40.

Kazalika yace sun samu nasarar kama tan sama da 9,000 na miyagun kwayoyin duka dai a cikin shekarar.

Maigatari ya yaba da kokarin jami’an hukumar, inda yace suna daukar kwararan matakai wajen kawar da dukkanin wani nau’i na tu’ammali da miyagun kwayoyi a fadin Kano, domin samar wa da al’ummar jihar zaman lafiya da kwanciyar hankali.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp