Home Labarai NDLEA ta kama sama da mutane dubu 1 a Kano

NDLEA ta kama sama da mutane dubu 1 a Kano

Hukumar dake hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa reshen jihar Kano NDLEA, tace ta samu nasarar cafke mutane 1,016 da ake zargin su da tu’ammali da miyagun kwayoyi a cikin shekarar 2023 da muka yi bankwana da ita.

Mai magana da yawun hukumar Sadiq Muhammad Maigatari shi ne ya bayyana hakan, inda yace mutanen da aka kama sun hadar da mata guda 40.

Kazalika yace sun samu nasarar kama tan sama da 9,000 na miyagun kwayoyin duka dai a cikin shekarar.

Maigatari ya yaba da kokarin jami’an hukumar, inda yace suna daukar kwararan matakai wajen kawar da dukkanin wani nau’i na tu’ammali da miyagun kwayoyi a fadin Kano, domin samar wa da al’ummar jihar zaman lafiya da kwanciyar hankali.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp