Sabon hari boko haram ya hallaka mutane 12 a Chibok

Wasu mutane sanye da kakin soji da ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne sun kashe mutane 12 a kauyukan Tsiha da kuma Gatamarwa da ke karamar hukumar Chibok a jihar Borno, Najeriya.

Mazauna kauyukan sun bayyana manema labarai cewa maharan sun dinga harbin mai uwa-da-wabi, lamarin da ya kai ga mutuwar mutanen, sannan suka yi awon gaba da mutum guda.

Rundunar ‘yan sandar jihar ta ce an samu gawarwakin mutanen da suka rasa rayukansu a harin.

Yayin da kuma ta fara bincike kan lamarin domin gurfanar da wadanda ake zargi da kai harin.

Bayanai sun nuna cewa maharan masu yawan gaske sun aukawa kauyukan ne a ranar Litinin da ta wuce.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 9 minutes 41 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 51 minutes 6 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com