Sabon hari boko haram ya hallaka mutane 12 a Chibok

Wasu mutane sanye da kakin soji da ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne sun kashe mutane 12 a kauyukan Tsiha da kuma Gatamarwa da ke karamar hukumar Chibok a jihar Borno, Najeriya.

Mazauna kauyukan sun bayyana manema labarai cewa maharan sun dinga harbin mai uwa-da-wabi, lamarin da ya kai ga mutuwar mutanen, sannan suka yi awon gaba da mutum guda.

Rundunar ‘yan sandar jihar ta ce an samu gawarwakin mutanen da suka rasa rayukansu a harin.

Yayin da kuma ta fara bincike kan lamarin domin gurfanar da wadanda ake zargi da kai harin.

Bayanai sun nuna cewa maharan masu yawan gaske sun aukawa kauyukan ne a ranar Litinin da ta wuce.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com