Wasu mutane sanye da kakin soji da ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne sun kashe mutane 12 a kauyukan Tsiha da kuma Gatamarwa da ke karamar hukumar Chibok a jihar Borno, Najeriya.
Mazauna kauyukan sun bayyana manema labarai cewa maharan sun dinga harbin mai uwa-da-wabi, lamarin da ya kai ga mutuwar mutanen, sannan suka yi awon gaba da mutum guda.
Read Also:
Rundunar ‘yan sandar jihar ta ce an samu gawarwakin mutanen da suka rasa rayukansu a harin.
Yayin da kuma ta fara bincike kan lamarin domin gurfanar da wadanda ake zargi da kai harin.
Bayanai sun nuna cewa maharan masu yawan gaske sun aukawa kauyukan ne a ranar Litinin da ta wuce.
PRNigeria hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 14 hours 44 minutes 34 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 16 hours 25 minutes 59 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com