Home Labarai NCC ta dakatar da shirin hana masu layin Glo kiran layin MTN

NCC ta dakatar da shirin hana masu layin Glo kiran layin MTN

Hukumar sadarwa ta Najeriya – NCC ta dakatar da shirin ta na hana masu amfani da layin kamfanin Glo kiran layukan kamfanin MTN na tsawon kwanaki ashirin ɗaya.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, Daraktan hulda da jama’a na hukumar NCC, Reuben Mouka, ya ce hukumar ta yanke shawarar dakatar da matakin ne bayan da kamfanonin sadarwa suka amince da warware duk wadansu matsalolin da ke tsakaninsu.

Tun da farko dai, hukumar ta ce ta amince da kamfanin MTN ya fara yanke kira da layin kamfanin Globacom daga ranar 18 ga Janairu, 2024, saboda takaddamar bashin da ya daɗe a tsakanin ɓangarorin.

“Hukumar ta yi farin cikin sanar da cewa a yanzu kamfanonin MTN da Glo sun cimma matsaya don warware duk wata matsala da ke tsakaninsu, saboda haka, hukumar ta dage dakatarwar da aka yi na tsawon kwanaki 21 daga yau 17 ga Janairu, 2024.

“A wajen bayar da amincewar hukumar, hukumar tana sane da illolin da shawarar za ta iya haifarwa ga masu amfani kamfanonin sadarwar biyu, don haka ta ci gaba da jan hankalin bangarorin biyu don saukaka wani kuduri wanda ya ba da fifiko da kuma kare muradun mabukaci da kuma tafiyar da harkokin sadarwa ta kasa baki daya,” in ji NCC.

“Yayin da hukumar ke sa ran MTN da Glo za su warware duk wata matsala da ta kunno kai a cikin kwanaki 21, hukumar ta ce dole ne duk kamfanonin da ke aiki su warware basussuka a matsayin wani abin da ya dace don bin ka’idojin doka na duk masu lasisi.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp