Home Labarai Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar kan Farouq...

Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar kan Farouq Lawan

Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar, kan tsohon dan majalisar Bagwai da shanono honarabul Farouk Lawan, bisa samun sa da laifin cin hanci na dalar amurka dubu dari biyar ($500,000).
Kotun Kolin ta tabbatar da Hukuncin Kotun kasa ne, wadda ta yankewa Farouk Lawan hukuncin zaman gidan yari na shekaru biyar, saboda samun sa laifin yana karbar cin hancin dala dubu dari biyar ($500,000), daga hannun wani dan kasuwa Femi Otedola.
Tunda fari dai an zargi Lawan da karbar cin hancin dala dubu dari biyar ($500,000) ne, a lokacin da majalisa take binciken tallafin man fetur a shekarar 2012.
Farouk Lawan dai ya daukaka karar ne tun a watan fabarairun shekarar 2022, inda ya roki kotun kolin ta soke hukuncin kotun daukaka karar dake Abuja, wadda tayi masa daurin shekaru biyar a gidan yari kan laifin farko, inda ta wanke shi akan sauran zarge-zargen guda biyu, wadanda gwamnatin Tarayya tayi kararsa akan zarge-zargen masu alaka da cin hanci da karbar rashawa.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp