Home General Kotun kolin Nijeriya ta tabbatar da Nasarar Gwamnonin Sokoto, Rivers da...

Kotun kolin Nijeriya ta tabbatar da Nasarar Gwamnonin Sokoto, Rivers da Taraba

Kotun koli ta tabbatar da zaɓen Ahmed Aliyu na jam’iyyar APC a matsayin halastaccen gwamnan jihar Sokoto.

Kotun koli a wani mataki na bai ɗaya ta yi watsi da ƙarar da Sa’idu Umar na jam’iyyar PDP ya shigar na ƙalubalantar nasarar Aliyu a zaɓen gwamna da aka gudanar a watan Maris na 2023.

wani labarin Kotun koli ta yi watsi da ɗaukaka karar da Tonye Cole, ɗan jam’iyyar APC ya shigar in da yake ƙalubalantar nasarar Siminalayi Fubara na jam’iyyar PDP a Zaɓen gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris na 2023 a jihar Rivers. Kotun ta tabbatar da Fubara a matsayin gwamnan jihar.

Kotun ta ce Cole bai tabbatar da zarginsa ba na cewa Fubara bai cancanta tsayawa takarar ba saboda bai bai yi murabus daga mukamin babban akanta janar na jihar Rivers ba kafin zaɓen wanda hakan ya saɓawa dokar zaɓe. Kotun ta ce karar da aka shigar bai yi nasara ba kuma ta yi watsi da shi.

haka kuma a wani labarin Kotun kolin ta tabbatar da zaɓen Agbu Kefas na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Taraba.

Kotun kolin a wani mataki na bai daya ta yi watsi da daukaka karar da Farfesa Yahaya Sani na jam’iyyar NNPP ya yi kan rashin cancantar Kefas tsayawa takarar gwamnan jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp