Home General Kotun kolin Nijeriya ta tabbatar da Nasarar Gwamnonin Sokoto, Rivers da...

Kotun kolin Nijeriya ta tabbatar da Nasarar Gwamnonin Sokoto, Rivers da Taraba

Kotun koli ta tabbatar da zaɓen Ahmed Aliyu na jam’iyyar APC a matsayin halastaccen gwamnan jihar Sokoto.

Kotun koli a wani mataki na bai ɗaya ta yi watsi da ƙarar da Sa’idu Umar na jam’iyyar PDP ya shigar na ƙalubalantar nasarar Aliyu a zaɓen gwamna da aka gudanar a watan Maris na 2023.

wani labarin Kotun koli ta yi watsi da ɗaukaka karar da Tonye Cole, ɗan jam’iyyar APC ya shigar in da yake ƙalubalantar nasarar Siminalayi Fubara na jam’iyyar PDP a Zaɓen gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris na 2023 a jihar Rivers. Kotun ta tabbatar da Fubara a matsayin gwamnan jihar.

Kotun ta ce Cole bai tabbatar da zarginsa ba na cewa Fubara bai cancanta tsayawa takarar ba saboda bai bai yi murabus daga mukamin babban akanta janar na jihar Rivers ba kafin zaɓen wanda hakan ya saɓawa dokar zaɓe. Kotun ta ce karar da aka shigar bai yi nasara ba kuma ta yi watsi da shi.

haka kuma a wani labarin Kotun kolin ta tabbatar da zaɓen Agbu Kefas na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Taraba.

Kotun kolin a wani mataki na bai daya ta yi watsi da daukaka karar da Farfesa Yahaya Sani na jam’iyyar NNPP ya yi kan rashin cancantar Kefas tsayawa takarar gwamnan jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp