Home Labarai Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar kan Farouq...

Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar kan Farouq Lawan

Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar, kan tsohon dan majalisar Bagwai da shanono honarabul Farouk Lawan, bisa samun sa da laifin cin hanci na dalar amurka dubu dari biyar ($500,000).
Kotun Kolin ta tabbatar da Hukuncin Kotun kasa ne, wadda ta yankewa Farouk Lawan hukuncin zaman gidan yari na shekaru biyar, saboda samun sa laifin yana karbar cin hancin dala dubu dari biyar ($500,000), daga hannun wani dan kasuwa Femi Otedola.
Tunda fari dai an zargi Lawan da karbar cin hancin dala dubu dari biyar ($500,000) ne, a lokacin da majalisa take binciken tallafin man fetur a shekarar 2012.
Farouk Lawan dai ya daukaka karar ne tun a watan fabarairun shekarar 2022, inda ya roki kotun kolin ta soke hukuncin kotun daukaka karar dake Abuja, wadda tayi masa daurin shekaru biyar a gidan yari kan laifin farko, inda ta wanke shi akan sauran zarge-zargen guda biyu, wadanda gwamnatin Tarayya tayi kararsa akan zarge-zargen masu alaka da cin hanci da karbar rashawa.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp