Home Labarai Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar kan Farouq...

Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar kan Farouq Lawan

Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar, kan tsohon dan majalisar Bagwai da shanono honarabul Farouk Lawan, bisa samun sa da laifin cin hanci na dalar amurka dubu dari biyar ($500,000).
Kotun Kolin ta tabbatar da Hukuncin Kotun kasa ne, wadda ta yankewa Farouk Lawan hukuncin zaman gidan yari na shekaru biyar, saboda samun sa laifin yana karbar cin hancin dala dubu dari biyar ($500,000), daga hannun wani dan kasuwa Femi Otedola.
Tunda fari dai an zargi Lawan da karbar cin hancin dala dubu dari biyar ($500,000) ne, a lokacin da majalisa take binciken tallafin man fetur a shekarar 2012.
Farouk Lawan dai ya daukaka karar ne tun a watan fabarairun shekarar 2022, inda ya roki kotun kolin ta soke hukuncin kotun daukaka karar dake Abuja, wadda tayi masa daurin shekaru biyar a gidan yari kan laifin farko, inda ta wanke shi akan sauran zarge-zargen guda biyu, wadanda gwamnatin Tarayya tayi kararsa akan zarge-zargen masu alaka da cin hanci da karbar rashawa.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp