Home Labarai Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar kan Farouq...

Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar kan Farouq Lawan

Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar, kan tsohon dan majalisar Bagwai da shanono honarabul Farouk Lawan, bisa samun sa da laifin cin hanci na dalar amurka dubu dari biyar ($500,000).
Kotun Kolin ta tabbatar da Hukuncin Kotun kasa ne, wadda ta yankewa Farouk Lawan hukuncin zaman gidan yari na shekaru biyar, saboda samun sa laifin yana karbar cin hancin dala dubu dari biyar ($500,000), daga hannun wani dan kasuwa Femi Otedola.
Tunda fari dai an zargi Lawan da karbar cin hancin dala dubu dari biyar ($500,000) ne, a lokacin da majalisa take binciken tallafin man fetur a shekarar 2012.
Farouk Lawan dai ya daukaka karar ne tun a watan fabarairun shekarar 2022, inda ya roki kotun kolin ta soke hukuncin kotun daukaka karar dake Abuja, wadda tayi masa daurin shekaru biyar a gidan yari kan laifin farko, inda ta wanke shi akan sauran zarge-zargen guda biyu, wadanda gwamnatin Tarayya tayi kararsa akan zarge-zargen masu alaka da cin hanci da karbar rashawa.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp