Home Labarai Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya aika sako zuwa ga Tinubu

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya aika sako zuwa ga Tinubu

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yayi kira ga Gwamnatin Tarayya data duba halinda Al’ummar Nigeria suke ciki na tsananin kunci kan hauhawar kayan abinci da rashin zaman lafiya a arewacin Kasar.

Sarkin yayi wannan kira ne a lokacin da Uwar gidan shugaban kasar Nijeriya Senator Remi Tunibu ta ziyarceshi a fadarsa dake gidan rumfa a jihar kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren masarautar Kano Abubakar Balarabe kofar Na’isa ya sanyawa hannu kuma aka raba ga manema labarai a jihar Kano

Alhaji Aminu Ado Bayero ya kara da cewa Senator Remi tayi kokari wajan fadada aikinta na alheri da takeyi a jahar kano dubada yawan Al’ummar da jihar take dasu.

Da take nata jawabin Uwar gidan Shugan kasar ta bayyanawa sarkin cewa tazo jihar kano ne domin tagodewa Al’ummar jihar bisa goyon bayan da suka bawa mijinta a lokacin zabe.

Daga karshe tayi alkawarin isar da sakon al’ummar Kano da Arewacin Nijeriya ga mai gidannata.

Uwar gidan shugaban kasar Senator Remi Tinubu tasamu rakiyar Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa na kasa Senator Barau Jibrin da Gwamnan jihar Benue da matar shugaban majalisar wakilai na kasa da Uwar gidan Gwamnan Kano.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp