Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya aika sako zuwa ga Tinubu

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yayi kira ga Gwamnatin Tarayya data duba halinda Al’ummar Nigeria suke ciki na tsananin kunci kan hauhawar kayan abinci da rashin zaman lafiya a arewacin Kasar.

Sarkin yayi wannan kira ne a lokacin da Uwar gidan shugaban kasar Nijeriya Senator Remi Tunibu ta ziyarceshi a fadarsa dake gidan rumfa a jihar kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren masarautar Kano Abubakar Balarabe kofar Na’isa ya sanyawa hannu kuma aka raba ga manema labarai a jihar Kano

Alhaji Aminu Ado Bayero ya kara da cewa Senator Remi tayi kokari wajan fadada aikinta na alheri da takeyi a jahar kano dubada yawan Al’ummar da jihar take dasu.

Da take nata jawabin Uwar gidan Shugan kasar ta bayyanawa sarkin cewa tazo jihar kano ne domin tagodewa Al’ummar jihar bisa goyon bayan da suka bawa mijinta a lokacin zabe.

Daga karshe tayi alkawarin isar da sakon al’ummar Kano da Arewacin Nijeriya ga mai gidannata.

Uwar gidan shugaban kasar Senator Remi Tinubu tasamu rakiyar Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa na kasa Senator Barau Jibrin da Gwamnan jihar Benue da matar shugaban majalisar wakilai na kasa da Uwar gidan Gwamnan Kano.

PRNigeria Hausa

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 8 minutes 10 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 49 minutes 35 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com