Home Labarai Kamfanin NNPC yace bazai kara kudin man Fetur a Nijeriya ba

Kamfanin NNPC yace bazai kara kudin man Fetur a Nijeriya ba

Kamfanin mai na Najeriya NNPC ya ce ba shi da shirin kara farashin man fetur a kasar duk kuwa kara tabarbarewar darajar takardar kudin Naira da ya haddasa tsadar rayuwa.

Karo na biyu kenan da Najeriyar ke karya darajar kudinta cikin kasa da shekara guda, lamarin da ya haddasa hauhawar farashin kayayyaki kari kan matsin rayuwar da jama’a ke fuskanta tun tuni, kuma wannan batu ya sanya fargabar karuwar farashin man na fetur, batun da kamfanin na NNPC ke cewa babu wannan shirin a yanzu.

Sanarwar ta NNPC na zuwa a dai dai lokacin da kiraye-kiraye ke ci gaba da tsananta daga kungiyoyi wajen ganin gwamnatin Najeriyar ta dauki matakan kawo sassauci kan matsin rayuwar da ake ciki, wadannan kungiyoyi kuwa har da na kwadago da suka bayar da wa’adin makwanni biyu ko kuma tsunduma yajin aiki.

A bangare guda kungiyar gwamnonin Najeriyar ta aikewa da gwamnatin tarayya bukatar gaggawa wajen magance matsalar ta tsadar rayuwa baya ga daidaita farashin Naira da kuma uwa uba magance matsalolin tsaron da arewacin kasar ke fama da shi.

A hukumance dai yanzu ana sayar da duk dalar Amurka guda kan Nairar Najeriyar dubu 1 da 531 sabanin 900 da ake sayarwa a makwannin baya, lamarin da ya sake tsawwala tsadar rayuwar da al’umma kef ama da shi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp