Home Labarai Kamfanin NNPC yace bazai kara kudin man Fetur a Nijeriya ba

Kamfanin NNPC yace bazai kara kudin man Fetur a Nijeriya ba

Kamfanin mai na Najeriya NNPC ya ce ba shi da shirin kara farashin man fetur a kasar duk kuwa kara tabarbarewar darajar takardar kudin Naira da ya haddasa tsadar rayuwa.

Karo na biyu kenan da Najeriyar ke karya darajar kudinta cikin kasa da shekara guda, lamarin da ya haddasa hauhawar farashin kayayyaki kari kan matsin rayuwar da jama’a ke fuskanta tun tuni, kuma wannan batu ya sanya fargabar karuwar farashin man na fetur, batun da kamfanin na NNPC ke cewa babu wannan shirin a yanzu.

Sanarwar ta NNPC na zuwa a dai dai lokacin da kiraye-kiraye ke ci gaba da tsananta daga kungiyoyi wajen ganin gwamnatin Najeriyar ta dauki matakan kawo sassauci kan matsin rayuwar da ake ciki, wadannan kungiyoyi kuwa har da na kwadago da suka bayar da wa’adin makwanni biyu ko kuma tsunduma yajin aiki.

A bangare guda kungiyar gwamnonin Najeriyar ta aikewa da gwamnatin tarayya bukatar gaggawa wajen magance matsalar ta tsadar rayuwa baya ga daidaita farashin Naira da kuma uwa uba magance matsalolin tsaron da arewacin kasar ke fama da shi.

A hukumance dai yanzu ana sayar da duk dalar Amurka guda kan Nairar Najeriyar dubu 1 da 531 sabanin 900 da ake sayarwa a makwannin baya, lamarin da ya sake tsawwala tsadar rayuwar da al’umma kef ama da shi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp