Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta sake bude kantin Sahad na Abuja

Gwamnatin Nijeriya ta sake bude kantin Sahad na Abuja

Hukumar da ke Kare Muradan Masu Saye ta Najeriya FCCPC ta sake buɗe katafaren kantin kayar da kayayyaki na Sahad Stores, bayan rufe shi.

A ranar Juma’a 16 ga watan Fabrairu ne hukumar ta garƙame babban kantin, saboda zargin yadda ake cuwa-cuwar sanya farashin kayayyaki a kantin.

Hukumar ta yi zargin cewa masu gudanar da katafaren kantin na ƙara wa abokan hulɗarsu kuɗin kaya fiye da farashin da ke maƙale a jikin kayan.

FCCPC ta ce hakan na tilasta wa kwantomomi biyan kuɗaɗe masu tsada don sayen kayayyaki.

To sai dai cikin wata sanarwa da mai riƙon muƙamin mataimakin shugaban hukumar, Adamu Abdullahi, ya fitar ya ce an sake buɗe kantin domin ci gaba da cinikayya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp